Aminiya:
2025-06-26@19:55:53 GMT

Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya

Published: 26th, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda ya bai wa Hukumar ƙididdiga ta jihar damar gudanar da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya a jihar.

Babban jami’in ƙididdiga na jihar, Farfesa Saifullahi Sani wanda ya bayyana hakan a Katsina ranar Alhamis, ya ce maƙasudin gudanar da ƙidayar shi ne tsara dabarun inganta tsarin.

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna An tallafawa iyalan ’yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno

Babban jami’in ƙididdigar ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taro na yini ɗaya da masu ruwa da tsaki a jihar.

Sani ya ce, “Manufofin ƙidayar sun haɗa da samar da cikakkun bayanai na dukkan Makarantun Alkur’ani da kuma samar da cikakken tsarin yaran da ba su zuwa makaranta a jihar.

“Manufofin hakan su ne, a tabbatar da halin da ɗaliban suke ciki, don sanin halin da suke ciki, da samun cikakkun bayanai na malaman makarantun.

“Haƙiƙa wannan an yi shi ne don samun cikakkun bayanai na ɗalibai a fannin.

“Haka kuma don tabbatar da adadin ɗaliban da suka tsunduma cikin harkar bara a jihar da kuma taimakawa wajen fahimtar hanyoyin aiwatarwa a halin yanzu, gano giɓi da jagoranci wajen samar da matakan da suka dace.”

Ya bayyana cewa, sakamakon ƙidayar zai sanar da shiga tsakani da kuma fara ƙoƙarin da suka dace na sauya tsarin karatun Alkur’ani a halin yanzu.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Almajirai Dikko Radda Makarantun Islamiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Da yake gabatar da kudirin, dan majalisar, Abdullahi ya nuna matukar damuwarsa kan kisan da aka yi wa matafiyan a ranar Juma’a, a lokacin da suka bata kan hanyarsu a yayin da suke tafiya don halartar wani daurin aure a karamar hukumar Mangu.

 

Ya ce, wadanda aka kashen, ba su dauke da wani makami, kawai suna kan hanyarsu ne ta zuwa daurin aure, wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari tare da kashe su, lamarin da ya jefa ‘yan uwan matafiyan cikin jimami.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato