Aminiya:
2025-08-11@03:51:05 GMT

Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja

Published: 26th, June 2025 GMT

An kama daya daga cikin mutanen da ake zargi da yin garkuwa da mutum uku a ƙauyen Daku da ke Gwagwalada Abuja lokacin da yake tsaka da cin kasuwar shanu ta Izom da ke Guraran jihar Neja.

Rahotanni sun ce a ranar tara ga watan Yunin 2025 ce dai aka sace wasu makiyaya su biyu da wani direba a kusa da kauyen na Daku.

An sace mutanen ne lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar ta Izom.

’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir

Mutanen da aka sace ɗin dai a wancan lokacin sai da suka biya kudin fansa har Naira miliyan 15 kafin su shaƙi iskar ’yanci.

Wani ɗan kungiyar sintiri ta bijilan a yankin, Ishaku Daniel, ya ce an cafke wanda ake zargi da garkuwa da mutanen ne wajen misalin karfe 4:00 na yamma a kasuwar bayan daya daga cikin waɗanda ya sace ya gane shi.

Ishaku ya ce an kama mutumin ne sanye da dogayen kaya lokacin da ya shigo kasuwar domin yin sayayya.

Ya ce nan take ’yan sintirin da ke kasuwar suka cika hannu da shi, duk da cewar jama’ar gari sun so su halaka shi a nan take.

Ya kuma ce ’yan sintirin sun sami fakiti-fakitin sigari da tiramol da maganin tari da kuma wiwi a cikin buhun wanda ake zargin.

Ishaku ya ce daga bisani sun mika shi ga jami’an tsaro da suka je kasuwar daga Lambata a jihar ta Neja.

Shi ma wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da kama mutumin, inda ya ce tuni ya amsa laifinsa yayin da ake ci gaba da bincike a kan lamarin.

Sai dai yunkurin wakilinmu na jin ta bakin Kakakin ’yan sandan jihar ta Neja, SP Wasiu Abiodun, a kan lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon shugaban jam’iyyar PDP kuma tsohon ministan noma daga 2015 zuwa 2019, Audu Ogbeh, ya rasu a ranar Asabar, 9 ga Agusta, yana da shekaru 78 a duniya, kamar yadda iyalinsa suka tabbatar.

A cikin wata sanarwa, iyalan sun ce: “Ya rasu cikin kwanciyar hankali, ya bar mana gado na gaskiya, hidima da jajircewa ga kasa da al’umma. Mun sami kwanciyar hankali daga yadda ya shafi rayuka da kuma yadda ya kafa misali.”

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

Iyalan sun bayyana cewa za a sanar da yadda za a gudanar da jana’izarsa a nan gaba, tare da godewa abokai, da abokan aiki. Sun kuma roƙi a basu dama domin yin jimamin rasuwar baban nasu.

Rahoton LEADERSHIP ya nuna cewa Ogbeh, wanda ya shahara a siyasa, rubuce-rubuce da aikin gona, ya shugabanci PDP daga 2001 zuwa 2005 kafin ya zama minista a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu
  • Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa
  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina