Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja
Published: 26th, June 2025 GMT
An kama daya daga cikin mutanen da ake zargi da yin garkuwa da mutum uku a ƙauyen Daku da ke Gwagwalada Abuja lokacin da yake tsaka da cin kasuwar shanu ta Izom da ke Guraran jihar Neja.
Rahotanni sun ce a ranar tara ga watan Yunin 2025 ce dai aka sace wasu makiyaya su biyu da wani direba a kusa da kauyen na Daku.
An sace mutanen ne lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar ta Izom.
’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik JingirMutanen da aka sace ɗin dai a wancan lokacin sai da suka biya kudin fansa har Naira miliyan 15 kafin su shaƙi iskar ’yanci.
Wani ɗan kungiyar sintiri ta bijilan a yankin, Ishaku Daniel, ya ce an cafke wanda ake zargi da garkuwa da mutanen ne wajen misalin karfe 4:00 na yamma a kasuwar bayan daya daga cikin waɗanda ya sace ya gane shi.
Ishaku ya ce an kama mutumin ne sanye da dogayen kaya lokacin da ya shigo kasuwar domin yin sayayya.
Ya ce nan take ’yan sintirin da ke kasuwar suka cika hannu da shi, duk da cewar jama’ar gari sun so su halaka shi a nan take.
Ya kuma ce ’yan sintirin sun sami fakiti-fakitin sigari da tiramol da maganin tari da kuma wiwi a cikin buhun wanda ake zargin.
Ishaku ya ce daga bisani sun mika shi ga jami’an tsaro da suka je kasuwar daga Lambata a jihar ta Neja.
Shi ma wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da kama mutumin, inda ya ce tuni ya amsa laifinsa yayin da ake ci gaba da bincike a kan lamarin.
Sai dai yunkurin wakilinmu na jin ta bakin Kakakin ’yan sandan jihar ta Neja, SP Wasiu Abiodun, a kan lamarin ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
Matar da ta daina ganin girman mijinta ta riga ta fara ruguza aurenta, da zarar kin yi masa maganganu na cin mutunci, kin yi kamar kin tozarta kanki da kanki ne, saboda girman mace a cikin aurenta yana da alaka da girman mijinta.
2. Rashin adalci tsakanin mijinki da danginsa
Ki sani, mijinki zai iya jure miki a kuskuren da kike masa kai tsaye, amma zai dade yana daukar zafin abin da kika aikata wa iyayensa, ‘yan uwansa ko danginsa, wannan babban kuskure ne da mata da dama suke yi su kuma yi nadama daga baya.
3. Rashin Tausayi da Kulawa
Ki sani, koda kuwa mijinki yana da kudi, yana bukatar jin tausayi daga gare ki. Idan ya dawo gida a gajiye, kuma ba kya nuna damuwarki ko kulawarki, hakan na iya sanyawa ya ji babu darajarsa a idonki. Wannan ma yana daga cikin manyan kurakuran da ake nadama a kai.
4. Yin kishi nai tauri da rashin amana
Kishin mace al’ada ne, amma idan ya wuce kima, yana canza soyayya zuwa guba. Idan baki yarda da mijinki ba, kina tuhumarsa a kan kowanne abu, to ke da kanki za ki gaji, shi ma ya gaji, sai aure ya fara tangal-tangal.
Za Mu Ci Gaba Mako Mai Zuwa In Allah Ya Kai Mu
ShareTweetSendShare MASU ALAKA