HausaTv:
2025-03-28@10:07:33 GMT

Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro

Published: 13th, March 2025 GMT

Kasashen Iran da Belarus, sun rattaba hannu kan wani daftari na bunkasa alaka ta haddin  guiwar tsaro a tsakaninsu.

Ministan tsaron kasar Iran Aziz Nasirzadeh da takwaransa na kasar Belarus Viktor Khrenin ne suka rattaba hannu kan wata takarda kan fadada hadin gwiwar tsaron kasashen biyu.

An rattaba hannu kan takardar ne a wata ganawar da ministocin biyu suka yi a Minsk, babban birnin kasar Belarus, inda bangarorin biyu suka kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi tsaro da kuma hanyoyin zurfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu da inganta hadin gwiwar soji.

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan batutuwan da suka shafi tsaro tare da yin musayar ra’ayi kan hanyoyin zurfafa dangantakar dake tsakaninsu.

A yayin wannan taron, ministan tsaron kasar ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro, musamman ta hanyar yin amfani da karfin kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da kasancewar kasashen biyu a cikin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, wajen tinkarar barazanar bai daya.

 Ya bayyana rattaba hannu kan wannan takarda a matsayin wani muhimmin mataki na karfafa huldar tsaro da tsaro tsakanin Tehran da Minsk.

A nasa bangaren, Janar Viktor Khrenin, ministan tsaron kasar Belarus, ya jaddada bukatar ci gaba da hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da tsaro mai dorewa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwar tsaro rattaba hannu kan

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye

A zantawa ta water tarho ministocin harkokin waje na kasashen Iran da Turkiya sun bukaci kasashen musulmi su magance matsalar jinkai da kayakin agaji na Falasdinawa a kasarsu da aka mamaye.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Hakan Fidan na kasar Turkiya da tokwaransa na kasar Iran Abbas Aragchi suna fadar haka a jiya Litinin.

A lokacinda yake Magana a kan rikicin da ke faruwa a kasar Turkiyya Abbas Aragchi ya bayyana cewa, rikici ne na cikin gida, kuma yana fatan gwamnatin kasar zara iya magancece ta yadda ta ga ya dace, kuma yana da imani zata iya magance matsalar.

Aragchi ya kara da cewa, wannan shi ne matsayin iran a cikin al-amuran da ke faruwa a kasashen yankin, ya kuma bayyana muhimmancin mutunta al-amuran da suka shafi cikin gida na ko wace kasa a yankin.

Sai kuma Hakan Fidan ministan harkokin wajen Turkiya  wanda ya sake jadda matsayin kasarsa  wajen neman hanyoyin diblomasiyya don warware matsalolin al-amuran Falasdinu da kasashen yankin da kuma sauran kasashen duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ƙwato wa mutumin da aka sace kuɗin fansarsa a Kano
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi
  • Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian
  • Kamfanonin Sin Za Su Samar Da Hidimomin Kyautata Amfani Da Makamashi Mai Tsafta A Afirka Ta Kudu
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Na Kano Ya Yi Murabus Watanni 7 Bayan Naɗa Shi
  • Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro