HausaTv:
2025-05-01@04:29:54 GMT

Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro

Published: 13th, March 2025 GMT

Kasashen Iran da Belarus, sun rattaba hannu kan wani daftari na bunkasa alaka ta haddin  guiwar tsaro a tsakaninsu.

Ministan tsaron kasar Iran Aziz Nasirzadeh da takwaransa na kasar Belarus Viktor Khrenin ne suka rattaba hannu kan wata takarda kan fadada hadin gwiwar tsaron kasashen biyu.

An rattaba hannu kan takardar ne a wata ganawar da ministocin biyu suka yi a Minsk, babban birnin kasar Belarus, inda bangarorin biyu suka kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi tsaro da kuma hanyoyin zurfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu da inganta hadin gwiwar soji.

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan batutuwan da suka shafi tsaro tare da yin musayar ra’ayi kan hanyoyin zurfafa dangantakar dake tsakaninsu.

A yayin wannan taron, ministan tsaron kasar ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro, musamman ta hanyar yin amfani da karfin kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da kasancewar kasashen biyu a cikin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, wajen tinkarar barazanar bai daya.

 Ya bayyana rattaba hannu kan wannan takarda a matsayin wani muhimmin mataki na karfafa huldar tsaro da tsaro tsakanin Tehran da Minsk.

A nasa bangaren, Janar Viktor Khrenin, ministan tsaron kasar Belarus, ya jaddada bukatar ci gaba da hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da tsaro mai dorewa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwar tsaro rattaba hannu kan

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai

A yammacin ranar Talata Arsenal ta karbi bakuncin PSG a matakin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

An dai barje gumi ne a filin wasa na Emirates, inda PSG ta yi wa Arsenal ci daya mai ban haushi har gida.

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

PSG ta fara cin ƙwallo ta hannun Ousmane Dembele a minti na huɗu da take leda, haka suka je hutu har da zagaye na biyu, amma Gunners ba ta farke ba.

Wannan shi ne karo na biyu da suka fuskanci juna a Champions League a kakar nan, inda Gunners ta yi nasarar cin 2-0 a Emirates a cikin watan Oktoba.

Arsenal da Paris Saint-Germain da Inter Milan da Barcelona su ne kungiyoyin da 4 da suka kai matakin zagayen daf da karshe na gasar.

A wannan Larabar ce kuma za a yi karon batta tsakanin Inter Milan da Barcelona, bayan kimanin shekara 15 da aka yi makamancin wannan karawar daf da karshe tsakanin ƙungiyoyin biyu a Gasar Zakarun Turai.

Inter Milan ce ta kai zagayen ƙarshe a 2010, sai dai wannan karon Barcelona na fatan lashe kofin bana da zarar ta fuskanci Arsenal ko Paris St Germain a watan gobe.

Sai dai, Barca da Inter sun fuskanci juna a gasar ta zakarun Turai a 2022/23, inda ta Italiya ta yi nasara 1-0 cikin Oktoban 2022 a wasa na biyu suka tashi 3-3 a Sifaniya.

Wannan shi ne karon farko da Barcelona ke fatan kai wa karawar ƙarshe a Champions League, tun bayan da ta lashe na biyar jimilla a 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya