Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro
Published: 13th, March 2025 GMT
Kasashen Iran da Belarus, sun rattaba hannu kan wani daftari na bunkasa alaka ta haddin guiwar tsaro a tsakaninsu.
Ministan tsaron kasar Iran Aziz Nasirzadeh da takwaransa na kasar Belarus Viktor Khrenin ne suka rattaba hannu kan wata takarda kan fadada hadin gwiwar tsaron kasashen biyu.
An rattaba hannu kan takardar ne a wata ganawar da ministocin biyu suka yi a Minsk, babban birnin kasar Belarus, inda bangarorin biyu suka kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi tsaro da kuma hanyoyin zurfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu da inganta hadin gwiwar soji.
A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan batutuwan da suka shafi tsaro tare da yin musayar ra’ayi kan hanyoyin zurfafa dangantakar dake tsakaninsu.
A yayin wannan taron, ministan tsaron kasar ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro, musamman ta hanyar yin amfani da karfin kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da kasancewar kasashen biyu a cikin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, wajen tinkarar barazanar bai daya.
Ya bayyana rattaba hannu kan wannan takarda a matsayin wani muhimmin mataki na karfafa huldar tsaro da tsaro tsakanin Tehran da Minsk.
A nasa bangaren, Janar Viktor Khrenin, ministan tsaron kasar Belarus, ya jaddada bukatar ci gaba da hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da tsaro mai dorewa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hadin gwiwar tsaro rattaba hannu kan
এছাড়াও পড়ুন:
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Ya kara da cewa yayin gudanar da aikin, jami’an hukumar sun gano babura hudu daga hannun wanda ake zargi babura uku na Jincheng da daya na Lifan Kumata, inda ya ce ana ci gaba da neman sauran abokan aikinsa biyu da suka tsere.
Haka kuma, ya bayyana cewa an kama mai safarar miyagun kwayoyi mai suna Salisu Abdullahi, dan shekara 28, mazaunin Semegu a Karamar Hukumar Kumbotso, a yankin Sabon Titin Dorayi, tare da tarin miyagun kwayoyi da ake zargin yana sayarwa don amfani na haram.
Kwayoyin da aka samo daga hannunsa sun hada da kwayoyi 100 na Padol 5mg, kwayoyi 30 na Pregabalin 300mg, kwayoyi 170 na Diazepam 10mg, da kuma kwaya guda daya ta karin karfin maza.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan kamun na cikin dabarun hukumar wajen rushe kungiyoyin masu aikata laifuka da ke da hannu a satar kayayyaki, lalata dukiyoyin jama’a da sauran miyagun ayyuka da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.”
Abdullahi ya ce ana ci gaba da bincike a kan wadanda ake zargi, kuma za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala binciken.
A ranar 6 ga Nuwamba, jaridar The PUNCH ta ruwaito cewa hukumar NSCDC ta Jihar Kwara ta kama mutane biyar bisa zargin satar igiyoyin wutar lantarki na transifoma da na fitilun titi a yankin Tanke da ke Ilorin.
Wadanda aka kama sun hada da Samson Akintola, Muhammed Zakariya, Mohammed Monsur, Ibrahim Hamida, da Kabir Abubakar.
An kama su ne da misalin karfe 1 na safe a ranar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025, yayin hadin gwiwar aikin jami’an NSCDC daga sashen Tanke Dibision da kuma Kungiyar Tsaro ta Bijilante ta al’ummar Tanke.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA