Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro
Published: 13th, March 2025 GMT
Kasashen Iran da Belarus, sun rattaba hannu kan wani daftari na bunkasa alaka ta haddin guiwar tsaro a tsakaninsu.
Ministan tsaron kasar Iran Aziz Nasirzadeh da takwaransa na kasar Belarus Viktor Khrenin ne suka rattaba hannu kan wata takarda kan fadada hadin gwiwar tsaron kasashen biyu.
An rattaba hannu kan takardar ne a wata ganawar da ministocin biyu suka yi a Minsk, babban birnin kasar Belarus, inda bangarorin biyu suka kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi tsaro da kuma hanyoyin zurfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu da inganta hadin gwiwar soji.
A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan batutuwan da suka shafi tsaro tare da yin musayar ra’ayi kan hanyoyin zurfafa dangantakar dake tsakaninsu.
A yayin wannan taron, ministan tsaron kasar ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro, musamman ta hanyar yin amfani da karfin kungiyoyin kasa da kasa, ciki har da kasancewar kasashen biyu a cikin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, wajen tinkarar barazanar bai daya.
Ya bayyana rattaba hannu kan wannan takarda a matsayin wani muhimmin mataki na karfafa huldar tsaro da tsaro tsakanin Tehran da Minsk.
A nasa bangaren, Janar Viktor Khrenin, ministan tsaron kasar Belarus, ya jaddada bukatar ci gaba da hadin gwiwar tsaro, domin tabbatar da tsaro mai dorewa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hadin gwiwar tsaro rattaba hannu kan
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
Sojojin kasar Iran sun cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan HKI a dazuda nan nan, wayo yau lahadi a ci gaba da musayar wauta da suke yi da sojojin HKI kwanaki uku da suka gabata.
Kamfanin dillancin labaran kare kai na kasar Iran Tasnim ya nakalto sojojin kasar na cewa sun cilla makamai masu linzami da Drones a karon farko da rana ido na ganin ido a kan HKI kuma tuna makaman sun fada a inda yakamata su fada a cikin haramtacciyar kasar.
A safiyar ranar jumma’a ce sojojin HKI suka kai hare-hare kan birnin Tehran inda suka kai manya-manyan jami’an sojojin kasar ga shahada, sannan suka kashe mutane fararen hula wadanda basu da laifi.
Bayan haka ne sojojin JMI suka fara maida martani a daren Asabar da daren lahadi, amma a wannan karon sun kai hare haren ne da ranar Lahadi ido na ganin ido.
Hare-haren wadanda aka basu suna “Alkawalin gaskiya Na 3 zasu ci gaba matakar HKI ta ci gaba da kaiwa Iran hare hare.