Leadership News Hausa:
2025-08-12@04:18:14 GMT

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

Published: 27th, June 2025 GMT

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

Duk da haka, a cikin ‘yan shekarun da suka wuce, rashin daidaituwa na jiki ya bayyana. Jami’ai sun fara fitar da takardun tambayoyi domin samun kudi a wasu kwanaki kafin a fara jarabawar, inda ‘yan kasuwa marasa kishi, dillalai, da malalata dalibai suka lalata shirin.

Wannan ya gurgunta kyawawan manufofin WAEC da ta bada fatawa da kuma kawo cikas ga ingancin takaddun shaida.

Abubuwan da suka faru na baya-bayan nan sun kara jaddada lalacewar tsarin ilimin kasar. Kusan wata guda da fitowar WASSCE, matsalar tsara JAMB ta tilasta wa dubban daliban UTME a jihohi shida da wasu sassan Legas yin jarrabawar bayan an basu maki kadan.

Wannan abin takaici ya sa wata daliba da abin ya shafa ta kashe kanta a Legas, sai dai daga baya hukumar ta JAMB ta yarda cewa babbar matsalar da aka samu gazawarta ce ba ta dalibai ba.

Shekarar 1970 ta kawo sauyi a koma bayan WAEC. Badakalar Owosho, inda wani jami’in hukumar ya fallasa amsar da dalibai suka yi a gaban jarrabawar, ya sa aka soke jarabawar a wasu cibiyoyi, wanda ya tilasta wa wadanda suka yi laifi da wadanda ba su ji ba gani ba su ci jarrabawar a shekara mai zuwa tare da kananan yaransu. Sai dai, sulhun da aka yi a shekarar 1977, wanda aka yi wa lakabi da ‘Edpo’ 77’, ya rufe rugujewar Owosho ta kowace fuska.

Dole ne WAEC ta fanshi kanta ta hanyar toshe madogarar da ma’aikatan da ba su da gaskiya suke ba da takardar tambayar ta. Dole ne ta gano tare da mika miyagu ga ‘yansanda domin gurfanar da su gaban kuliya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: WAEC

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

An sake shiga tashin hankali a Jihar Sakkwato bayan wani sabon mummunan hari da ’yan bindiga suka kai a wasu kauyuka, lamarin da ke ƙara tsananta matsalar tsaro a faɗin jihar.

Rahotanni sun nuna cewa duk shekara musamman a lokacin damina, ’yan bindiga sukan ƙara ƙaimi wajen kai hare-haren da ke tarwatsa jama’a a garuruwansu da hana manoma zuwa gona ko kuma ƙaƙaba musu harajin zuwa gonakin.

An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi Dan wasan Barcelona Inigo Martinez ya koma Al-Nassr

Aminiya ta ruwaito cewa, a bana ma, maharan sun ci gaba da addabar mazauna ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 na Jihar Sakkwato.

Majiyoyi sun tabbatar cewa a harin baya-bayan nan, ’yan ta’addan sun hallaka mutane da dama sannan sun yi garkuwa da wasu.

Shafin Bakatsine da ke bibiyar rahotannin da suka shafi sha’anin tsaro, a wannan Lahadin ya wallafa a manhajar X cewa, an kai hari a wani masallaci a garin Bushe da ke Karamar Hukumar Sabon Birni, inda aka sace aƙalla mutum 10 ciki har da limamin masallacin.

Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.

Haka kuma, rahotanni sun ce maharan sun sake kai wani hari a lokacin sallar Isha a ƙauyen Marnona na Karamar Hukumar Wurno, a daren Asabar, inda suka kashe masallata da dama sannan suka yi awon gaba da wasu.

Sanata Ibrahim Lamido, mai wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa, ya yi Allah wadai da hare-haren da suka auku a Bushe da Marnona, inda ya buƙaci hukumomi su ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyar al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • Tehran: Kasar Lebanon Tana Da yencin Kare Kanta Da Makamanta
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
  • Ana Alhinin Tunawa Da Harin Nukiliyar Nagasaki Shekarau 80 Da Suka Gabata A Japan