Leadership News Hausa:
2025-10-13@17:09:45 GMT

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

Published: 27th, June 2025 GMT

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

Duk da haka, a cikin ‘yan shekarun da suka wuce, rashin daidaituwa na jiki ya bayyana. Jami’ai sun fara fitar da takardun tambayoyi domin samun kudi a wasu kwanaki kafin a fara jarabawar, inda ‘yan kasuwa marasa kishi, dillalai, da malalata dalibai suka lalata shirin.

Wannan ya gurgunta kyawawan manufofin WAEC da ta bada fatawa da kuma kawo cikas ga ingancin takaddun shaida.

Abubuwan da suka faru na baya-bayan nan sun kara jaddada lalacewar tsarin ilimin kasar. Kusan wata guda da fitowar WASSCE, matsalar tsara JAMB ta tilasta wa dubban daliban UTME a jihohi shida da wasu sassan Legas yin jarrabawar bayan an basu maki kadan.

Wannan abin takaici ya sa wata daliba da abin ya shafa ta kashe kanta a Legas, sai dai daga baya hukumar ta JAMB ta yarda cewa babbar matsalar da aka samu gazawarta ce ba ta dalibai ba.

Shekarar 1970 ta kawo sauyi a koma bayan WAEC. Badakalar Owosho, inda wani jami’in hukumar ya fallasa amsar da dalibai suka yi a gaban jarrabawar, ya sa aka soke jarabawar a wasu cibiyoyi, wanda ya tilasta wa wadanda suka yi laifi da wadanda ba su ji ba gani ba su ci jarrabawar a shekara mai zuwa tare da kananan yaransu. Sai dai, sulhun da aka yi a shekarar 1977, wanda aka yi wa lakabi da ‘Edpo’ 77’, ya rufe rugujewar Owosho ta kowace fuska.

Dole ne WAEC ta fanshi kanta ta hanyar toshe madogarar da ma’aikatan da ba su da gaskiya suke ba da takardar tambayar ta. Dole ne ta gano tare da mika miyagu ga ‘yansanda domin gurfanar da su gaban kuliya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: WAEC

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa

Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar  Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.

Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.

DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja

Wannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.

A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.

Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.

Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.

A watan Yuli 2025  Gwamna Umar Namadi ya gudanar da  bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar  Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.

Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara  tsaurara matakan tsaro da kuma samar da  tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da  zubar da jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano