Aminiya:
2025-06-25@11:43:34 GMT

DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Published: 25th, June 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Da za a kirkiri sabuwar jiha a Najeriya a yanzu, to da dole a samar da karin gwamna daya da sabuwar majalisar dokoki, da sababbin ma’aikatun gwamnati, da sauransu.

Samar da wadannan kuwa abu ne da yake bukatar makudan kudi – akalla Naira biliyan 30 duk shekara.


Ko da jihar za ta iya sama wa kanta kudin shiga kuma, za ta bukaci tallafi daga Gwamnatin Tarayya kafin ta tsaya da kafafunta.
Shin a halin matsin tattalin arzkin da take fuskanta yanzu, Najeriya tana da kudin da za ta reni sababbin jihohi kuwa?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan abin da kirkirar sababbin jihohi a Najeriya yake nufi ta fuskar tattalin arziki.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kirkirar sabbin jihohi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 

Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Bayelsa, Ebiyerin Omukoro.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Asabar a unguwar Ekeki, kusa da babban titin Melford Okilo a Yenagoa, babban birnin jihar.

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Rahotanni sun bayyana cewa, mutanen sun isa a cikin mota ƙirar Hilux, sanye da baƙaƙen kaya.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, maharsn sun kutsa kai gidan cin abincin da alƙalin ke ciki kuma suka tilasta masa shiga motarsu.

Har zuwa yanzu, ba a san inda suka kai shi ba, kuma babu wani saƙo ko buƙatar kuɗin fansa daga masu garkuwar.

Hakazalika ba a san dalilin da ya sa suka sace shi ba.

Wannan ba shi ne karon farko da aka sace mutum a yankin ba, domin an je har gida an sace wani ɗan jarida mai suna Oyins Egrenbido.

Wasu hotuna da bidiyo da suka karaɗe shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka kama alƙalin tare da jefa shi cikin motar ƙirar Hilux.

Har yanzu Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bayelsa, ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da sace alƙalin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
  • NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
  • Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
  • Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
  • NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • ’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa