Aminiya:
2025-06-26@13:21:35 GMT

2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau

Published: 26th, June 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya ce zai karɓi kowane irin muƙami da Shugaba Bola Tinubu ya ba shi, amma ya ce a yanzu ba ya son a yi magana kan batun zama mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Yayin wata ganawa da manema labarai kan shirin sauraron ra’ayoyin jama’a da za a yi kan sauya kundin tsarin mulki, Barau ya ce, “Duk abin da Shugaba ya ce na yi, zan yi shi da yaƙini na gaske.

Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su

Wannan na zuwa ne bayan ya shawarci wani rukuni da ke goyon bayan ya zama mataimakin shugaban ƙasa da su mayar da hankali wajen tallafa wa ayyukan Tinubu maimakon batun siyasa.

Ya ce, “Yin wannan magana a yanzu bai dace ba. Ban san waɗannan mutane ba, amma na gode da yadda suka yarda da ni.

“Na faɗa musu su daina ɓata lokaci kan abin da lokacisa bai yi ba, su yi amfani da kuɗinsu da ƙarfinsu wajen tallafa wa Shugaban Ƙasa.”

“Idan lokacin siyasa ya yi, za mu shiga. Amma yanzu lokaci ne na aiki.”

Barau ya bayyana Shugaba Tinubu a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ce yana yi wa biyayya.

Ya gode masa saboda taimakonsa wajen warware rikicin jam’iyya a Kano, dawowarsa majalisa a 2023, da kuma tallafa masa ya zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa.

“Ina son na sanar da ku, idan Shugaba ya ce yana buƙatar na yi aiki tare da shi, zan ce masa ‘na gode sosai,’ kuma zan yi. Duk abin da ya buƙaci na yi, zan yi shi. Zan yi masa biyayya. Shi ne uban ƙasa, kun sani.”

Barau, ya ce su dukkaninsu ’yan jam’iyyar APC ne, kuma suna da ra’ayoyi iri ɗaya.

“Mun fito daga gida ɗaya, mun sadaukar da kanmu ga ci gaba. Ina da ra’ayin ganin an samu ci gaba. Don haka zan yi wa Shugaban Ƙasa cikakkiyar biyayya. A 2027, duk abin da ya ce na yi, zan yi.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanata Barau Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta

Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Isra’ila da Iran, bayan zargin ƙasashen biyu da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla.

Lamarin na zuwa ne bayan ɓullar rahoton kai wa juna hari daga dukkan ƙasashen biyu, duk da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ’yan sa’o’in da suka gabata.

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya

Trump ya ce ƙasashen sun daɗe suna faɗa da juna, kuma a wannan mataki ana iya cewa ba su ma san abin da suke yi ba.

Ya ce: “Ba abin da muke so ke nan ba, ina tabbatar muku cewa ina fushi da abin da suka aikata.”

Shugaba Trump ne mutum na farko da ya fara sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ilan da Iran, bayan shafe kwana 12 suna kai wa juna hare-hare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
  • Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC
  • Mun amince da tsagaita wuta da Iran —Isra’ila
  • An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027