Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
Published: 26th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda ya bai wa Hukumar ƙididdiga ta jihar damar gudanar da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya a jihar.
Babban jami’in ƙididdiga na jihar, Farfesa Saifullahi Sani wanda ya bayyana hakan a Katsina ranar Alhamis, ya ce maƙasudin gudanar da ƙidayar shi ne tsara dabarun inganta tsarin.
Babban jami’in ƙididdigar ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taro na yini ɗaya da masu ruwa da tsaki a jihar.
Sani ya ce, “Manufofin ƙidayar sun haɗa da samar da cikakkun bayanai na dukkan Makarantun Alkur’ani da kuma samar da cikakken tsarin yaran da ba su zuwa makaranta a jihar.
“Manufofin hakan su ne, a tabbatar da halin da ɗaliban suke ciki, don sanin halin da suke ciki, da samun cikakkun bayanai na malaman makarantun.
“Haƙiƙa wannan an yi shi ne don samun cikakkun bayanai na ɗalibai a fannin.
“Haka kuma don tabbatar da adadin ɗaliban da suka tsunduma cikin harkar bara a jihar da kuma taimakawa wajen fahimtar hanyoyin aiwatarwa a halin yanzu, gano giɓi da jagoranci wajen samar da matakan da suka dace.”
Ya bayyana cewa, sakamakon ƙidayar zai sanar da shiga tsakani da kuma fara ƙoƙarin da suka dace na sauya tsarin karatun Alkur’ani a halin yanzu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai Dikko Radda Makarantun Islamiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokokin Yawon Buɗe Ido da Zartar da Shari’a
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci da nufin ƙarfafa harkar yawon buɗe ido da hanzarta gudanar da shari’a a faɗin jihar.
Shugaban majalisar, Yusuf Dahiru Liman, ne ya sanar da amincewar majalisar yayin zaman, ta wanda aka gudanar a harabar majalisar da ke Kaduna.
Dokar farko mai taken “Dokar Kafa Hukumar Kula da Yawon Buɗe Ido, Gidajen Tarihi, Shata Wurare, Lambuna da Wuraren Hutu na Jihar Kaduna, 2024”, na da nufin bunƙasa harkar yawon buɗe ido da raya al’adu a jihar.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Yusuf Dahiru Liman
Da yake gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Harkokin Fasaha, Shari’a da Ilimi, Magaji Suleiman, ya bayyana cewa kwamitin ya gudanar da cikakken bincike kan kudirin kuma ya fahimci cewa yana da amfani wajen haɓaka yawon buɗe ido da al’adu.
Magaji Suleiman ya ce idan aka fara aiki da hukumar, za ta inganta shata wurare, lambuna da wuraren shakatawa a jihar, wanda hakan zai ja hankalin masu zuba jari daga cikin gida da waje.
A nasa jawabin, wanda ya dauki nauyin gabatar da kudirin, Mr. Henry Marah, ya bayyana cewa hukumar za ta taka rawa wajen farfaɗo da al’adun gargajiya na jihar Kaduna wacce ke da yawan kabilu daban daban.
Ya ƙara da cewa dokar za ta taimaka wajen samar da kuɗaɗen shiga ga jihar, ƙirƙiro guraben ayyukan yi ga matasa da kuma cusa tarbiyar al’adu ga matasa masu tasowa.
Barista Emmanuel Kantiyok
Har ila yau, Majalisar ta kuma amince da gyara dokar gudanar da shari’ar laifuka ta Jihar Kaduna ta shekarar 2017.
Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, Barista Emmanuel Kantiyok, ya bayyana cewa gyaran dokar zai taimaka wajen gudanar da shari’a a kan lokaci da kuma tabbatar da adalci ba tare da la’akari da matsayin mutum ba.
Barista Kantiyok ya ce gyaran dokar zai taimaka wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma ƙara wa talakawa kwarin gwiwa ga tsarin shari’a.
Majalisar ta amince da dokokin ne ta hanyar ƙuri’ar murya da ‘yan majalisar suka kada, karkashin jagorancin Shugaban Majalisar, Yusuf Dahiru Liman.
Daga ƙarshe, majalisar ta tafi hutu kuma za ta dawo zaman ta a ranar 9 ga Satumba, 2025.
Shamsuddeen Mannir Atiku