’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe
Published: 27th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta samu nasarar kama wasu ɓarayin daji da suka addabi garin Bajoga da ke Ƙaramar Hukumar Funakaye.
Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen yaƙar masu aikata laifuka a faɗin jihar.
Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?A wata sanarwa da Kakakin Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa an kama mutum huɗu da ake zargi da kai wa wani matashi mai suna Muhammed Ahmed hari, wanda ke zaune a Unguwar Matasa, Bajoga.
An ce ɓarayin sun kai masa hari da makami cikin dare, inda suka tsoratar da shi da adda da sanduna, suka kuma ƙwace masa kayayyaki.
Sanarwar ta ce laifin ya faru da sanyin safiyar ranar 26 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 1:30 na dare.
Sun shiga gidan Ahmed ɗauke da makamai, suka kuma yi masa barazana da cewa za su kashe shi idan bai biya musu buƙata ba.
Waɗanda ake zargi da aikata wannan laifi sun haɗa da Manu Muhammed da ake kira (Bappa Charger), Auwalu Muhammed da ake kira (Yellow) mai shekaru 30 daga Bajoga.
Sauran sun haɗa da Ubaida Sani mai shekaru 19 daga Unguwar Pantami a Gombe, da Hussaini Muhammed mai shekaru 19 daga Unguwar Madaki, Gombe.
DSP Buhari, ya ce yayin da ake gudanar da bincike, ’yan sanda sun ƙwato babur ƙirar Haojue UD wanda kuɗinsa ya Naira miliyan 1.6, wayoyi uku da kuɗinsu ya kai Naira 336,000, tsabar kuɗi Naira 74,150, da kuma wuƙa.
Ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin suna hannun ’yan sanda yanzu, kuma bincike na ci gaba da gudana.
Ya ce da zarar an kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɓarayi zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya ce ko sisi gwamnati ba ta biya waɗanda suka yi garkuwa da ɗalibai mata 25 na sakandaren gwamnati ta Maga da ke jihar ba.
Ya bayyana hakan ne a taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar a ranar Talata, inda ya tabbatar da kubutar da ɗaliban da aka sace a farkon makon nan.
Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a KebbiYa ce, “An karɓo ɗalibanmu da aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya ba jami’an tsaro umarni su gano inda yaran suke, kuma su kubutar da su. Muna tabbatar wa iyayen yara da al’ummar Kebbi cewa ’ya’yansu sun dawo lafiya.
“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro, musamman sojoji, ’yan sanda, da Civil Defence da suka yi aiki tukuru har aka kubutar da yaran cikin ƙoshin lafiya,” in ji Gwamnan.
Idris ya jaddada cewa gwamnatin Kebbi ba ta biya kuɗin fansa ba, “Mu, a matsayin gwamnati, ba mu ba da ko sisi ba. A binciken da muka yi, babu wanda ya biya kuɗin fansar yaran.”
A ranar Litinin din da ta gabata ce ’yqn bindiga suka sace ɗaliban su 25 daga makarantar bayan sun kashe mataimakin shugaban makarantar.
Sai dai daga bisani ɗaya daga cikin ɗaliban ta gudo ’yan kwanaki bayan sace su.