Aminiya:
2025-06-27@18:20:14 GMT

’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Published: 27th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta samu nasarar kama wasu ɓarayin daji da suka addabi garin Bajoga da ke Ƙaramar Hukumar Funakaye.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen yaƙar masu aikata laifuka a faɗin jihar.

Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?

A wata sanarwa da Kakakin Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa an kama mutum huɗu da ake zargi da kai wa wani matashi mai suna Muhammed Ahmed hari, wanda ke zaune a Unguwar Matasa, Bajoga.

An ce ɓarayin sun kai masa hari da makami cikin dare, inda suka tsoratar da shi da adda da sanduna, suka kuma ƙwace masa kayayyaki.

Sanarwar ta ce laifin ya faru da sanyin safiyar ranar 26 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 1:30 na dare.

Sun shiga gidan Ahmed ɗauke da makamai, suka kuma yi masa barazana da cewa za su kashe shi idan bai biya musu buƙata ba.

Waɗanda ake zargi da aikata wannan laifi sun haɗa da Manu Muhammed da ake kira (Bappa Charger), Auwalu Muhammed da ake kira (Yellow) mai shekaru 30 daga Bajoga.

Sauran sun haɗa da Ubaida Sani mai shekaru 19 daga Unguwar Pantami a Gombe, da Hussaini Muhammed mai shekaru 19 daga Unguwar Madaki, Gombe.

DSP Buhari, ya ce yayin da ake gudanar da bincike, ’yan sanda sun ƙwato babur ƙirar Haojue UD wanda kuɗinsa ya Naira miliyan 1.6, wayoyi uku da kuɗinsu ya kai Naira 336,000, tsabar kuɗi Naira 74,150, da kuma wuƙa.

Ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin suna hannun ’yan sanda yanzu, kuma bincike na ci gaba da gudana.

Ya ce da zarar an kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɓarayi zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma

A ƙoƙarinta na bunƙasa noma da samar da isasshen abinci, Gwamnatin Jihar Gombe ta amince ta sayi tan 10,000 na taki, wanda ya yi daidai da buhu 200,000 domin shirin noman daminar bana.

Kwamishinan Harkokin Noma na Jihar, Dokta Barnabas Musa Malle, ya ce za a kashe Naira biliyan 8.8 wajen sayen takin.

1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau

Ya ce hakan na nuna yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tallafa wa manoma da kuma ƙara samar da abinci a jihar.

Dokta Malle ya ce, “Gwamnati ta fito da sabbin hanyoyin aiki sama da yadda aka yi a baya, kuma za a raba wa manoma takin domin su fara amfani da shi kafin damina ta sauka.”

Ya kuma bayyana cewa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya zai ƙaddamar da wannan shiri a ranar Alhamis, 26 ga watan Yuni, 2025.

An shirya sayar da takin a farashi mai rahusa domin manoma su iya saya.

Wannan shiri yana daga cikin matakan gwamnatin na tabbatar da ci gaba a harkar noma da kuma shawo kan matsalar ƙarancin abinci a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
  • Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?