Aminiya:
2025-08-12@04:10:23 GMT

’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Published: 27th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta samu nasarar kama wasu ɓarayin daji da suka addabi garin Bajoga da ke Ƙaramar Hukumar Funakaye.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen yaƙar masu aikata laifuka a faɗin jihar.

Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?

A wata sanarwa da Kakakin Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa an kama mutum huɗu da ake zargi da kai wa wani matashi mai suna Muhammed Ahmed hari, wanda ke zaune a Unguwar Matasa, Bajoga.

An ce ɓarayin sun kai masa hari da makami cikin dare, inda suka tsoratar da shi da adda da sanduna, suka kuma ƙwace masa kayayyaki.

Sanarwar ta ce laifin ya faru da sanyin safiyar ranar 26 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 1:30 na dare.

Sun shiga gidan Ahmed ɗauke da makamai, suka kuma yi masa barazana da cewa za su kashe shi idan bai biya musu buƙata ba.

Waɗanda ake zargi da aikata wannan laifi sun haɗa da Manu Muhammed da ake kira (Bappa Charger), Auwalu Muhammed da ake kira (Yellow) mai shekaru 30 daga Bajoga.

Sauran sun haɗa da Ubaida Sani mai shekaru 19 daga Unguwar Pantami a Gombe, da Hussaini Muhammed mai shekaru 19 daga Unguwar Madaki, Gombe.

DSP Buhari, ya ce yayin da ake gudanar da bincike, ’yan sanda sun ƙwato babur ƙirar Haojue UD wanda kuɗinsa ya Naira miliyan 1.6, wayoyi uku da kuɗinsu ya kai Naira 336,000, tsabar kuɗi Naira 74,150, da kuma wuƙa.

Ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin suna hannun ’yan sanda yanzu, kuma bincike na ci gaba da gudana.

Ya ce da zarar an kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɓarayi zargi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta cafke wasu mutane shida da ake zargin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane ne a karamar hukumar Doma da ke jihar.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Ramhan Nansel ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a lafiya, ya ce jami’an sun kuma kama wani makiyayi dauke da makamai a karamar hukumar Keana ta jihar.

 

Sanarwar ta ce, jami’an sashin Doma da ke aiki da sahihan bayanan sirri daga wani dan kasa mai kishin kasa, karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan shiyya, sun kai samame a wata maboyar ‘yan ta’adda da ke Yelwa Ediya inda aka kama wadanda ake zargin.

 

Ya ce a yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin yin garkuwa da wani kansila mai ci inda suka sace wayoyin hannunsa guda biyu.

 

Sun kuma amince da cewa sun tare hanyar Doma zuwa Yelwa ne inda suka kai hari kan wani Ibrahim Haruna Yelwa Ediya tare da kwace babur dinsa kirar Bajaj wanda kudinsa ya kai ₦970,000 yayin da ake sayar da babur din da suka sace.

 

SP Ramhan Nansel ya bayyana cewa, a yayin aikin jami’an sun kwato kudi ₦100,000 – kudaden da aka siyar da babur din da aka binne a daji, tare da babur Bajaj daya.

 

A wani labarin makamancin haka, jami’an sashin Keana sun amsa kiran da suka yi na cewa makiyayan da ke kiwo a filayen gonaki a Gidan Zaki Hassan da ke karamar hukumar Kuduku a karamar hukumar Keana, yayin da makiyayan suka yi ta harbe-harbe kafin su gudu.

 

‘Yan sandan da ke aiki da jama’ar gari sun kama wani makiyayi mai shekaru 20, sannan sun kwato bindiga samfurin AK-47 guda daya dauke da harsashi guda shida.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin mika duk wadanda ake tuhuma zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.

 

CP Mohammed ya jaddada kudirin rundunar na tabbatar da zaman lafiya ga kowa da kowa, yana mai gargadin cewa ba za a samu mafaka ga masu aikata laifuka ba.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda kuma su ci gaba da bayar da bayanai masu inganci a kan lokaci don taimakawa ayyukan ‘yan sanda.

 

Rel/Aliyu Muraki/Lafia.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Karɓi Ƙarin Kasafin Kuɗi Na 2025
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu
  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya