Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
Published: 26th, June 2025 GMT
Ɗaya daga cikin baƙin da suka tafi ɗaurin aure daga Zariya, Abbas Rufa’i, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga harin da wasu matasa suka kai musu a Ƙaramar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato.
A cewarsa, “Da muka tsaya a hanya domin yin tambaya, na fito daga motar domin neman hanya. Amma sai na ga yadda mutanen da ke wajen suka fara mana wani irin kallo.
“Na ji ɗaya daga cikinsu yana cewa, ‘a kashe su gaba ɗaya, a ƙone motar.’”
Rufa’i ya ƙara da cewa, “Na cire rigata, na shiga cikin daji har na sai da na samu wani mai babur, na ce masa ya kai ni wajen ‘yan sanda. Amma da muka isa wajen wasu sojoji, sai na ce ya tsaya, na sanar da su abin da ya faru.”
Ya bayyana cewa sojojin sin bi shi zuwa wajen, inda suka ceto mutane 18 da suka jikkata, yayin da wasu sun rasu.
Za mu biya diyya – Gwamnatin FilatoKwamishinar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato, Joyce Ramnap, ta ce gwamnati za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.
Ta ce, “Za mu biya diyya. Amma muna jiran rahoton ‘yan sanda kafin mu ɗauki mataki.”
’Yan majalisa sun buƙaci a kama waɗanda suka aikata laifinMajalisar Wakilai ta buƙaci Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Shugaban DSS da Hafsan Sojin Ƙasa su kama waɗanda suka aikata kisan.
Hon. Sadiq Ango Abdullahi ya ce, “Rashin kama masu laifi yana ƙara kawo rashin gaskiya da ƙarancin amana ga gwamnati.”
Kowa yana da ’yancin yin tafiya — Gwamna Uba Sani
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce, “Doka ta bai wa kowa ’yancin zirga-zirga a Najeriya. Gwamnoni su tabbatar da hakan.”
Ya godewa al’ummar Kudan da suka zauna lafiya duk da irin halin da suka tsinci kansu a ciki.
Za a hukunta waɗanda suka aikata laifin – Gwamnatin FilatoJoyce Ramnap ta ce an kama mutum 22 da ake zargi da hannu a harin. “Za mu hukunta duk wanda aka samu da laifi,” in ji ta.
Wannan laifi abu ne da aka tsara — Ƙungiyar Musulmai
Ƙungiyar Musulmai ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta ce, “Ba kuskure aka yi ba. Wannan kisan an shirya shi ne. Idan ba a hukunta masu laifin ba, hakan na iya jawo ramuwar gayya.”
Waɗanda suka aikata wannan laifi dabbobi ne — Ƙungiyar CANƘungiyar Kiristoci ta Arewa ta ce, “Kisan da aka yi wa waɗanda ba su da laifi ba shi ne mafi muni cikin ɗabi’ar ɗan Adam. Wannan rashin imani ne kuma bai dace ba.”
Wannan kisan laifi ne da aka shirya — Ƙungiyar Dattawan ArewaNEF ta ce, “Wannan ba kuskure ba ne, laifi ne da aka tsara. Yana nuna irin matsalolin da ke damun Arewa.”
Ƙungiyar ta buƙaci a hukunta duk masu hannu cikin lamarin.
Kisan ’yan ɗaurin auren da suka taso daga garin Zariya zuwa Filato, ya tayar da ƙura a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke Allah-wadai da kisan.
Yanzu haka dai an zuba wa jami’an tsaro da gwamnati ido don ganin irin matakin da za a ɗauka kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Ɗaurin Aure diyya gwamnati hari Jami an Tsaro Tsira Zariya waɗanda suka aikata
এছাড়াও পড়ুন:
Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya ce ko sisi gwamnati ba ta biya waɗanda suka yi garkuwa da ɗalibai mata 25 na sakandaren gwamnati ta Maga da ke jihar ba.
Ya bayyana hakan ne a taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar a ranar Talata, inda ya tabbatar da kubutar da ɗaliban da aka sace a farkon makon nan.
Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a KebbiYa ce, “An karɓo ɗalibanmu da aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya ba jami’an tsaro umarni su gano inda yaran suke, kuma su kubutar da su. Muna tabbatar wa iyayen yara da al’ummar Kebbi cewa ’ya’yansu sun dawo lafiya.
“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro, musamman sojoji, ’yan sanda, da Civil Defence da suka yi aiki tukuru har aka kubutar da yaran cikin ƙoshin lafiya,” in ji Gwamnan.
Idris ya jaddada cewa gwamnatin Kebbi ba ta biya kuɗin fansa ba, “Mu, a matsayin gwamnati, ba mu ba da ko sisi ba. A binciken da muka yi, babu wanda ya biya kuɗin fansar yaran.”
A ranar Litinin din da ta gabata ce ’yqn bindiga suka sace ɗaliban su 25 daga makarantar bayan sun kashe mataimakin shugaban makarantar.
Sai dai daga bisani ɗaya daga cikin ɗaliban ta gudo ’yan kwanaki bayan sace su.