Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
Published: 26th, June 2025 GMT
Ɗaya daga cikin baƙin da suka tafi ɗaurin aure daga Zariya, Abbas Rufa’i, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga harin da wasu matasa suka kai musu a Ƙaramar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato.
A cewarsa, “Da muka tsaya a hanya domin yin tambaya, na fito daga motar domin neman hanya. Amma sai na ga yadda mutanen da ke wajen suka fara mana wani irin kallo.
“Na ji ɗaya daga cikinsu yana cewa, ‘a kashe su gaba ɗaya, a ƙone motar.’”
Rufa’i ya ƙara da cewa, “Na cire rigata, na shiga cikin daji har na sai da na samu wani mai babur, na ce masa ya kai ni wajen ‘yan sanda. Amma da muka isa wajen wasu sojoji, sai na ce ya tsaya, na sanar da su abin da ya faru.”
Ya bayyana cewa sojojin sin bi shi zuwa wajen, inda suka ceto mutane 18 da suka jikkata, yayin da wasu sun rasu.
Za mu biya diyya – Gwamnatin FilatoKwamishinar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato, Joyce Ramnap, ta ce gwamnati za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.
Ta ce, “Za mu biya diyya. Amma muna jiran rahoton ‘yan sanda kafin mu ɗauki mataki.”
’Yan majalisa sun buƙaci a kama waɗanda suka aikata laifinMajalisar Wakilai ta buƙaci Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Shugaban DSS da Hafsan Sojin Ƙasa su kama waɗanda suka aikata kisan.
Hon. Sadiq Ango Abdullahi ya ce, “Rashin kama masu laifi yana ƙara kawo rashin gaskiya da ƙarancin amana ga gwamnati.”
Kowa yana da ’yancin yin tafiya — Gwamna Uba Sani
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce, “Doka ta bai wa kowa ’yancin zirga-zirga a Najeriya. Gwamnoni su tabbatar da hakan.”
Ya godewa al’ummar Kudan da suka zauna lafiya duk da irin halin da suka tsinci kansu a ciki.
Za a hukunta waɗanda suka aikata laifin – Gwamnatin FilatoJoyce Ramnap ta ce an kama mutum 22 da ake zargi da hannu a harin. “Za mu hukunta duk wanda aka samu da laifi,” in ji ta.
Wannan laifi abu ne da aka tsara — Ƙungiyar Musulmai
Ƙungiyar Musulmai ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta ce, “Ba kuskure aka yi ba. Wannan kisan an shirya shi ne. Idan ba a hukunta masu laifin ba, hakan na iya jawo ramuwar gayya.”
Waɗanda suka aikata wannan laifi dabbobi ne — Ƙungiyar CANƘungiyar Kiristoci ta Arewa ta ce, “Kisan da aka yi wa waɗanda ba su da laifi ba shi ne mafi muni cikin ɗabi’ar ɗan Adam. Wannan rashin imani ne kuma bai dace ba.”
Wannan kisan laifi ne da aka shirya — Ƙungiyar Dattawan ArewaNEF ta ce, “Wannan ba kuskure ba ne, laifi ne da aka tsara. Yana nuna irin matsalolin da ke damun Arewa.”
Ƙungiyar ta buƙaci a hukunta duk masu hannu cikin lamarin.
Kisan ’yan ɗaurin auren da suka taso daga garin Zariya zuwa Filato, ya tayar da ƙura a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke Allah-wadai da kisan.
Yanzu haka dai an zuba wa jami’an tsaro da gwamnati ido don ganin irin matakin da za a ɗauka kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Ɗaurin Aure diyya gwamnati hari Jami an Tsaro Tsira Zariya waɗanda suka aikata
এছাড়াও পড়ুন:
An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Legas ta yi wa wasun ‘yan China shida ɗaurin shekara ɗaya bayan ta same su da laifin ta’addanci da zamba ta intanet.
Sanarwar da hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin Nijeriya ta’annati (EFCC) ta fitar ta ce kotun da ke unguwar Ikoyi ta Jihar Legas ce ta ɗaure mutanen ne bayan ta same su da laifi.
Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO“Masu laifin sun hada da : JIA You (da aka fi sani da A. You) da Wang Zheng Feng ( da aka fi sani da Feng) da Liu San Hua da Chen Wen Yuan da Liu BeiIxingda Wen Zong Xu (da aka fi sani Li Long),” in ji sanarwar.
EFCC ta ce masu laifin suna cikin mutum 792 da ake zargi da hannu a damfara ta hanyar kirifto waɗanda aka kama ranar 19 ga watan Disamba shekarar 2024 a Legas a wani samame da hukumar ta ƙaddamar mai taken “Eagle Flush Operation.”
Bayan an kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotu kan zargin aikata ta’addanci da kuma aikata zamba ta intanet.
Sanarwar ta ambato tuhumar da aka yi wa masu laifin na shiga manhajar komfuta da gangan domin lalata tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Nijeriya, wanda hakan ya nuna cewa ya aikata laifi da ya saɓa wa dokar hana laifukan intanet ta 2015 da kuma dokar hana ta’addanci ta 2022.
Daga farko dai waɗanda ake zargin sun musanta zargin da aka karanta musu daga takardar tuhumar.
Sai dai kuma a zaman kotun na ranar 23 ga watan Yuni sun sauya matsayarsu zuwa amsa laifi, kuma nan take lauyoyin gwamnati suka nemi kotu ta same su da laifi tare da hukunta su.
“Saboda haka, kotun ta same su da laifi tare da yi wa kowanne daga waɗanda ake tuhumar ɗaurin shekara ɗai-ɗai daga ranar 10 ga watan Disamba na shekarar 2025, da kuma cin kowanne daga cikinsu tarar naira miliyan ɗaya-ɗaya,” in ji sanarwar.
Alƙalin ya kuma ba da umarni ga shugaban hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya ya tabbatar cewa an mayar da ’yan China ƙasar da suka fito cikin kwanani bakwai da zarar sun kammala wa’adin gidan yari.
Kazalika, kotun ta ba da umarnin cewa a sallamar da wayoyi da kamfutoci da kuma na’uororin samar da intanet da aka ƙwace daga masu laifin wa Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.