Ofishin kula da aikin harba kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin ya ba da labari cewa, jiya Alhamis da karfe 9 da mintuna 29 na dare agogon Beijing, ‘yan sama jannatin kumbon Shenzhou-20, wato Chen Dong da Chen Zhongrui da Wang Jie sun cimma nasarar fitowa daga akwatin gwaji na Wentian, yin tattaki a waje na tsawon sa’o’i 6.

5, da kuma komawa akwatin, bisa taimakon na’urori masu hannun injin dake tashar sararin samaniya da jagorancin masu nazarin kimiyya da fasaha dake doron kasa.

Yayin da suke aiki a waje, Chen Dong da Chen Zhongrui sun cimma nasarar hada na’urorin kiyaye tashar sararin samaniya daga sassan wasu na’urorin da aka daddasa a sararin samaniya, da binciken na’urorin dake waje da tashar da daidaita wasu matsaloli da sauransu.

Ya zuwa yanzu, ‘yan sama jannatin suna tafiyar da ayyukansu bi da bi yadda ya kamata, daga baya kuma za su yi nazari da gudanar da aikin gwaji kan bangaren kimiyyar rayuka da tushen samuwar karamar fizga ko “jazibiyya” da kimiyyar albarkatun sararin samaniya da aikin jinya a sararin samaniya da sabbin kimiyya da fasahohin zirga-zirga a sararin samaniya da sauransu. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sararin samaniya da

এছাড়াও পড়ুন:

Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya nesanta kansa daga wata kungiya da take fafutukar ganin Shugaban Kasa Bola Tinubu ya dauke shi a matsayin mataimakinsa a 2027.

Mai magana da yawun Sanatan, Isma’il Mudashir ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata, inda ya ce a maimakon haka, kamata ya yi kungiyar ta fi mayar da hankali wajen mara wa Tinubu baya ya samu nasarar yunkurinsa na bunkasa Najeriya.

A kwanan nan ne dai wata kungiya mai suna Zauren Matasan APC na Arewacin Najeriya (NNPYA) ta ayyana goyon bayanta ga Tinubu ya dauki Sanatan a matsayin wanda za su yi takara tare.

Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha

Hakan dai ya biyo bayan jita-jitar da ake ta yadawa a ’yan kwanakin nan cewa ba lallai ne Tinubun ya sake yin takara tare da Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a 2027 din ba.

A cewar Sanata Barau, “An jawo hankalina kan wasu rubuc-rubuce a shafukan sada zumunta da ma wasu jaridu na wasu kungiyoyi, cikinsu har da NNPYA, inda suke kiran jagoranmu, Shugaba Bola Tinubu, da ya dauke ni a matsayin mataimaki a 2027. Wannan ba da yawuna ba ne kuma ba shi ne abu mafi muhimmanci ba a yanzu.

“Ina kira ga NNPYA da ma sauran kungiyoyin da ke wannan fafutukar da su daina daga yanzu, sannan su mayar da hankalinsu wajen goyon bayan yunkurin Shugaba Tinubu na magance matsalolin da ke addabar kasarmu.

“Kamata ya yi mu hada karfi da karfe wajen goyon bayan Tinubu har ya samu ya kai Najeriya tudun mun tsira.

“Yanzu ba lokaci ne da za mu rika wannan kiraye-kirayen ba, lokaci ne na tabbatar da cewa Tinubu ya samu nasarar sauke nauyin da ke wuyansa.

“Ya damu kwarai da gaske wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba. Saboda haka nake kira da kowa ya goya masa baya kan kudurorinsa da tuni aka fara ganin amfaninsu a kasa,” in ji Sanata Barau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Bejjo Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027