Aminiya:
2025-07-09@07:41:11 GMT

Dan ta’adda zai biya tarar miliyoyi bayan shan dukan kawo wuka a Katsina

Published: 12th, March 2025 GMT

Wani dan bindiga da ya karya yarjejeniyar sulhu a Karamar Hukumar Jibiya ta Jihar Katsina mai suna Bala Wuta na Garin Mazanya, na can kwance rai-kwakwai-mutu-kwakwai bayan ya sha dukan kawo wuka.

Tubabbun ’yan bindiga sun yi wa Bala wuta takakkiya ne har gida inda suka yi masa bugun dawa, bayan da ya yi garkuwa da wasu matafiya jim kadan bayan sulhun da aka yi, inda bayan sun lugwiwita shi, suka wajabta masa biyan tarar Naira miliyan uku.

HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas

Ana iya tuna cewa, a ranar 28 ga watan Fabrairu, 2025 ne aka yi sulhun, wanda ya samu wakilcin sojoji da ’yan sanda da sauran jami’an tsaro da masu ruwa karkashin jagorancin shugaban karamar hukumar ta Jibiya Alhaji Maitan, kamar yadda su ’yan bindigar suka nema.

’Yan bindigar da suka halarci zaman a karkashin jagoransu Audu Lankai, sun hada da Kantoma da Ori da Tukur Dan Najeriya da Bammi da sauransu da suka fito daga yankin Zamfara.

Yarjejeniyar da aka kulla

Jama’ar yankin sun shimfida wa ’yan bindiga sharadin barin kai hare-hare a fadin karamar hukumar da hanyar Katsina zuwa Jibiya da hanyar Jibiya zuwa Gurbi da kuma wadda ke zuwa Batsari.

Za kuma su da daina kai hari ko barna a gonaki ko cikin daji ko guje-guje a kan babura a cikin garin ko nuna rashin da’a ko tarbiyya ga al’umma.

Kazalika, yarjejeniyar ta bukaci za su kiyaye duk dokokin gwamnati su kuma daina yawo da makamai a bainar jama’a.

A nasu bangaren, tubabbun ’yan bindigar dajin sun shardanta a daina kashe su ko kama dabbobinsu babu dalili da kuma tabbatar da adalci a tsakaninsu da sauran al’umma a matsayinsu na ’yan kasa.

Sa’annan sun bukaci a daina daukar doka da hannu a rika barin hukuma ta yi hukunci ga mai laifi.

Bayan nan ne suka sako mutane 10 na garin Daddara da ke hannunsu tare da mika bindiga kirar AK-49 guda biyu.

Bala Wuta ya ji a jikinsa

Sai dai duk da wannan yarjejeniyar sulhu da aka kulla, sai ga shi a ranar Alhamis da ta gabata, wani wanda bai shiga sulhun ba mai suna Bala Wuta na Garin Mazanya da ya addabi hanyar zuwa Jibiya, ya kayar da wata mota ya yi awon gaba da matafiya a Mallamawar Batsari — garin su Lankai.

A dalilin haka shi Audu Lankai jagoran sasanci ya taras da shi har gida ya yi mishi dukan kawo wuka sannan ya sanya masa tarar kudi har naira milyan uku.

Har zuwa yanzu, wakilinmu ya ruwaito cewa, Bala Wuta yana can kwance yana jin jiki a garin na Mazanya.

Labarin da muka samu daga garin na Jibiya an ce, a ranar Lahadi an ga Fulanin da ke cikin dajin sun shigo kasuwa mazansu da matansu cikin murna saboda samun wannan ’yanci.

Majiyarmu ta shaida mana cewa, Fulanin sun rika sayen lemon kwalba mai sunyi da ake sayarwa Naira 250, wanda suke cewa a can daji naira dubu ake sayar musu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jibiya yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kamfanin dillancin labarun “Reutres” ya bayyana cewa; Cibiyar da take tafiyar da ayyukan agaji a Gaza, wacce Amurka ta kafa ta, ta bayar da wata shawarar da take cewa; a kafa wa mutanen Gaza hemomi na wucin gadi da za su zama masomin yin hijirarsu zuwa wani wuri daban, a cikin yankin ko a wejensa.

Rahoton kamfanin dillancin labarun na Reuters ya ambato wata majiya mai karfi tana cewa; An gabatarwa da shugaban kasar Amurka shawarar tilastawa mutanen Gaza yin hijira, kuma a cikin kwanakin nan an tatauna wannan batu a fadar mulkin Amurka ta “White House.”

Har ila yau rahoton ya kunshi cewa,tun daga watan Febrairu cibiyar ta fara kokarin tara kudaden da za su kai dalar Amurka biliyan 1 domin aiwatar da Shirin hijirar mutanen Gaza a cikin yankin ko kuma zuwa wajensa, da kuma kwace makaman da suke a hannun ‘yan gwagwarmaya.

A karkashin wannan Shirin da akwai matakai guda uku; Na farko shi ne bayar da kayan agaji. Na biyu shi ne gina hemomi na tsugunar da Falasdinawa a cikinsu. Na uku shi ne fitar da mutanen Gaza zuwa hijira ta dole, wacce babu dadowa.

 A fili yake cewa a cikin matakin farko da har yanzu ake cikinsa, wurin da aka kira na raba kayan agaji, ba komai ba ne,sai tarko na kashe Faladinawa. Duk wanda ya je domin ya karbi kayan agaji, to ya zama abin farautar ‘yan sahayoniya.

Masu kula da wadannan cibiyoyin na agaji da aka kafa kuwa su ne; HKI da wata rundunar sojojin ‘yan ina da yaki ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – Radda
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato
  • Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 
  • Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan