Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
Published: 25th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya sanya wa sabuwar gadar sama da aka kammala a Lafia, Babban Birnin Jihar, sunan Shugaba Bola Tinubu.
Gwamnan, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ƙaddamar da aikin a Lafia.
’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a KanoYa ce an gina gadar bisa tsarin Shugaba Tinubu, kuma an kammala aikin ne ba tare da ciyo bashi ba, sakamakon inganta amfani da kuɗin gwamnati.
Sabuwar gadar mai tsawon kilomita ɗaya, wadda ke da gadar sama da ƙasa, na ɗauke da sunan ‘Bola Tinubu Exchange Road’.
A wajen buɗe aikin, Shugaba Tinubu ya gode wa Gwamna Sule bisa jajircewarsa wajen aiwatar da ayyukan da ke taimaka wa rayuwar al’umma.
Haka kuma, ya nuna farin cikinsa da irin tarbar da ya samu daga mutanen Nasarawa.
Sannan ya yi kira a gare su da su ci gaba da mara wa gwamnati baya wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gadar Sama Gwamna Sule Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Ya bayyana cewa, gwamnatin da ta gabata ce ta rufe cibiyoyin da aka kafa a gwamnatin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, amma gwamnatinsa ta yanke shawarar farfado da su domin magance matsalar rashin aikin yi.
“Don haka ne a yau, kowane Dalibi wanda ya kammala karatun, ba kawai takardar shaida za a bashi ba har ma da kayan aikin sana’ar da ya koya” in ji Yusuf.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp