Aminiya:
2025-06-26@13:12:55 GMT

Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir

Published: 26th, June 2025 GMT

Shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Jama’atul Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), Sheik Sani Yahaya Jingir, ya ce ba zai goyi bayan takarar Bola Tinubu ba a zaben 2027 matukar ya canza Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron wa’azi a masallacinsa na ’Yan Taya da ke Jos, babban birnin jihar Filato.

Aminiya ta rawaito cewa a zaben 2023 da ya gabata dai Sheikh Jingir ya goyi bayan Tinubu sannan ya umarci magoya bayansa da su ma su yi haka a wancan lokacin.

Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump

Jita-jitar da ake yadawa dai a kan cewa akwai yiwuwar Tinubu ya ajiye Kashim din a matsayin abokin takararsa a zabe mai zuwa ta dada kamari a ’yan kwanakin nan.

To sai dai da yake nasa tsokacin a kan batun, malamin addinin ya ce, “Na ji akwai wasu mutane marasa kishin kasa daga ciki da wajen APC da ke kokarin lalata alakar da ke tsakanin Tinubu da Kashim domin cimma mummunar manufarsu. To mu ba ma maraba da wannan Shugaba Tinubu.

“Ni da wasu na kusa da ni mun goyi bayan Tinubu da Kashim, kuma za mu sake goyon bayan takararku a tare. Duk wani yunkuri sabanin haka ba na tare da shi kuma ba zan goyi baya ba saboda a baya sun amince su yi aiki tare.

“Na goyi bayansu ba tare da sun ba ni ko sisi ba. duk da yake ina da kusanci da Atiku, amma na ce Tinubu da Kashim zan yi. Akwai jita-jitar da ke yawo cewa dangantaka ta yi tsami a tsakaninsu, amma ni ban yarda da, na fi tunanin aikin makiya ne,” in ji malamin.

Sheikh Jingir ya kuma yi kira ga Shugba Tinubu da kada ya saurari masu kiran nasa da ya ajiye Kashim ya canza shi da wani a 2027, inda ya bayyana wadannan mutanen a matsayin marasa son ci gaba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya ce an ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta gaba daya a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.

Kafar yaɗa labarai ta the Guardian ta ƙasar Birtaniya ta ruwaito cewa Trump ya sanar da haka ne a shafinsa na sadar da zamunta, ’yan sa’o’i bayan hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kai a sansanin sojin Amurka da ke ƙasar Qatar da Iran bayan hare-haren da Amirkan ta kai wa Iran.

Ya sanar cewa cikin awa shida na farko Iran za ta fara dakatar da kai hare-hare, daga bisani Isra’ila ta dakatar, wanda hakan zai kawo ƙarshen yaƙin ɗungurungum.

Sanarwar tasa na zuwa ne bayan tsohon Fira Ministan Rasha, babbar ƙawar Iran, Dimitry Medvedev na cewa ƙasashe masu ƙarfin makaman nukiliya na yi wa Iran tayin makaman nasu a yayin da yaƙin ke ƙara ƙamari.

Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha

Kazalika akwai yiwuwar babbar abokiyar gaban Amurka, wato Koriya ta Kudu na shirin taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da hare-haren Amurka da Isra’ila suka shafa, da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya.

Hakan na zuwa ne kuma bayan Majalisar Dokokin Iran ta amince da ƙudirin rufe mashigar tekun Hormuz, matakin da Amurka ta buƙaci China ta sa baki Iran ɗin ta janye.

A gefe guda kuma Iran ta ci gaba da ruwan rokoki a kan Isara’ila, wadda ta fara kai wa cibiyoyin nukiliyar da na harkokin soji da fararen hula hari a ranar 13 ga watan nan na Yuni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi
  • An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki