Leadership News Hausa:
2025-06-26@19:51:41 GMT

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Published: 26th, June 2025 GMT

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Adedeji ya ce har zuwa sa’o’i biyu kafin sanarwar, sunan hukumar shi ne FIRS, amma yanzu sunan ya koma NRS.

Ya bayyana cewa sabuwar hukumar ba za ta tsaya kan tattara haraji kawai ba, domin yanzu tana damar tattara sauran kuɗaɗen shiga da ba na haraji ba.

Hakazalika, za ta yi aiki cikin ’yanci tare da bin ƙa’idojin bayyanan aiki da bin diddigin nasarori.

Ya ƙara da cewa sabuwar hukumar za ta mayar da hankali sosai wajen cimma nasarori, kuma za ta yi aiki da ƙwarewa kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya.

Shi ma shugaban kwamitin gyaran haraji na fadar shugaban ƙasa, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa ko da kuwa doka na da kyau, idan ba a aiwatar da ita yadda ya kamata ba, ba za ta amfanar da ƙasa ba.

Ya ce yanzu shugaban ƙasa ya umarce su da su fara aiki yadda ya kamata.

Oyedele ya ja hankalin jama’a cewa wannan gyara ba zai yi nasara ba sai kowa ya bayar da gudunmawarsa.

Ya ce gwamnati kaɗai ba za ta iya aiwatar da wannan sauyi ba.

Dole ne a samu haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, ƙungiyoyin fararen hula, ƙwararru, da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa.

Shugaba Tinubu tun da farko ya ce dokokin harajin an tsara su ne don gina ƙasa, tare da kawar da ɓarna da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.

Wannan gyaran haraji yana cikin babban shirin gwamnatinsa da ke neman kyautata yanayin kasuwanci, ƙara samun kuɗaɗen shiga, da kuma ganin ci gaba ya waanzu a faɗin ƙasar.

Yanzu da aka sa ranar fara amfani da dokokin a Janairun 2026, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suna da lokaci don shirya duk abin da ya kamata domin tabbatar da cewa sabbin dokokin harajin sun cika burinsu na kawo ci gaba ga ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Haraji Tsari

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.

 

Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su.
Sai dai a wannan zamani ‘yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikin su ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita.
Ko wadanne matakai ya kamata ‘yan Najeriya su ringa dauka wajen kare kan su da ma lafiyar jikin su?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A YAU na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda ‘yan Najeriya zasu dinga kula da lafiyar jikin su.

Domin sauke shirn, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
  • Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 
  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC
  • An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027