Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir

Shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Jama’atul Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), Sheik Sani Yahaya Jingir, ya ce ba zai goyi bayan takarar Bola Tinubu ba a zaben 2027 matukar ya canza Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron wa’azi a masallacinsa na ’Yan Taya da ke Jos, babban birnin jihar Filato.

Aminiya ta rawaito cewa a zaben 2023 da ya gabata dai Sheikh Jingir ya goyi bayan Tinubu sannan ya umarci magoya bayansa da su ma su yi haka a wancan lokacin.

Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump

Jita-jitar da ake yadawa dai a kan cewa akwai yiwuwar Tinubu ya ajiye Kashim din a matsayin abokin takararsa a zabe mai zuwa ta dada kamari a ’yan kwanakin nan.

To sai dai da yake nasa tsokacin a kan batun, malamin addinin ya ce, “Na ji akwai wasu mutane marasa kishin kasa daga ciki da wajen APC da ke kokarin lalata alakar da ke tsakanin Tinubu da Kashim domin cimma mummunar manufarsu. To mu ba ma maraba da wannan Shugaba Tinubu.

“Ni da wasu na kusa da ni mun goyi bayan Tinubu da Kashim, kuma za mu sake goyon bayan takararku a tare. Duk wani yunkuri sabanin haka ba na tare da shi kuma ba zan goyi baya ba saboda a baya sun amince su yi aiki tare.

“Na goyi bayansu ba tare da sun ba ni ko sisi ba. duk da yake ina da kusanci da Atiku, amma na ce Tinubu da Kashim zan yi. Akwai jita-jitar da ke yawo cewa dangantaka ta yi tsami a tsakaninsu, amma ni ban yarda da, na fi tunanin aikin makiya ne,” in ji malamin.

Sheikh Jingir ya kuma yi kira ga Shugba Tinubu da kada ya saurari masu kiran nasa da ya ajiye Kashim ya canza shi da wani a 2027, inda ya bayyana wadannan mutanen a matsayin marasa son ci gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu
  • An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
  • CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026