Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
Published: 27th, June 2025 GMT
Babban malamin addinin Islama kuma jagoran mabiya Darikar Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya cika shekaru 101 a duniya, a lissafin kalandar Musulunci.
An haifi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ne a ranar 2 ga watan Muharram a shekara ta 1346 bayan hijira, inda a gobe Juma’a, 2 ga Muharram na shekarar 1447, yake cika shekaru 101 cif a ban kasa.
Duk da cewa iyalai da almajiran Maulana Shehu Dahiru Usman Bauchi ba su yi wani biki don taya shi murnar cika shekara 100 a duniya, amma masoya da almajiran Shehin Malamin sun bayyana farin cikinsu da yi masa addu’o’i musamman a dandali daban-daban na shafukan Intanet.
Sun yaba da irin hidimar da ya yi wa Musulunci da Bil Adama, inda suka jinjina rawar da ya taka a matsayinsa na shugaba mai kishi da kuma tsayuwar daka.
Daya daga cikin almajiransa, Malam Ahmad Tijjani Saeed ya ce, “Yayin da Maulana Sheikh yake cika shekaru 101 cikin koshin lafiya, ya bar abin koyi mai tarin yawa a rayuwa wajen bauta wa Allah da hidimta wa al’ummarsa da kuma bil’adama.”
Sauran almajiran irinsu Malam Ahmad Tijjani Kolo, Sanusi Ahmad, da Muhammad Sogiji, sun yaba wa jajircewar Sheikh Bauchi wajen yin magana kan zalunci da azzalumai da kuma matsalolin zamantakewa kamar cin hanci da rashawa, kungiyoyin asiri, da shaye-shayen miyagun kwayoyi.
Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda babban jigo a Darikar Tijjaniyya a Nijeriya da Afirka, shi ne Mataimakin Shugaban Kwamitin Fatawa na Majalisar Koli kan Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya.
Babban malamin na da ’ya’ya kimanin 100 da jikoki 406, da tattaba-kunne 100, wadanda su ma suka gaje shi a fannin haddar Al-Qur’ani.
Abin sha’awa, 78 daga cikin ’ya’yansa da jikoki sama da 199, da tattaba kunne 12 su ma sun haddacce Al-Kur’ani, hadi da ilimin boko da na addinin Musulunci.
Sheikh Bauchi ya yi aikin Hajji sau 56 da Umrah sau 207.
Hidimar Al-QuraniSheikh Bauchi ya fara Tafsirinsa ne a Jihar Bauchi a shekarar 1948, kuma ya shafe shekaru 77 wajen yin tafsirin Alkur’ani mai girma.
An fara yada Tafsirinsa a gidan rediyon Bauchi a shekarar 1976, kafin daga baya gidan rediyon Najeriya Kaduna ya fara yadawa a 1980.
A halin yanzu, gidajen rediyo da dama a arewacin Najeriya suna yada koyarwarsa, musamman a cikin watan Ramadan.
KaratunsaYa fara karatunsa na Musulunci ne a hannun mahaifinsa, Alhaji Usman, inda ya haddacce Alkur’ani mai girma tun kafin ya cika shekara 20 a duniya.
Ya ci gaba da karatunsa a karkashin manya malaman Musulunci na ciki da wajen Najeriya, inda Sheikh Ibrahim Inyass ya kasance babban malaminsa.
A halin yanzu Sheikh Bauchi yana zaune ne a Kofar Gombe da ke birnin Bauchi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Adedeji ya ce har zuwa sa’o’i biyu kafin sanarwar, sunan hukumar shi ne FIRS, amma yanzu sunan ya koma NRS.
Ya bayyana cewa sabuwar hukumar ba za ta tsaya kan tattara haraji kawai ba, domin yanzu tana damar tattara sauran kuɗaɗen shiga da ba na haraji ba.
Hakazalika, za ta yi aiki cikin ’yanci tare da bin ƙa’idojin bayyanan aiki da bin diddigin nasarori.
Ya ƙara da cewa sabuwar hukumar za ta mayar da hankali sosai wajen cimma nasarori, kuma za ta yi aiki da ƙwarewa kamar yadda ake yi a sauran ƙasashen duniya.
Shi ma shugaban kwamitin gyaran haraji na fadar shugaban ƙasa, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa ko da kuwa doka na da kyau, idan ba a aiwatar da ita yadda ya kamata ba, ba za ta amfanar da ƙasa ba.
Ya ce yanzu shugaban ƙasa ya umarce su da su fara aiki yadda ya kamata.
Oyedele ya ja hankalin jama’a cewa wannan gyara ba zai yi nasara ba sai kowa ya bayar da gudunmawarsa.
Ya ce gwamnati kaɗai ba za ta iya aiwatar da wannan sauyi ba.
Dole ne a samu haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, ƙungiyoyin fararen hula, ƙwararru, da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa.
Shugaba Tinubu tun da farko ya ce dokokin harajin an tsara su ne don gina ƙasa, tare da kawar da ɓarna da kuma bunƙasa tattalin arziƙi.
Wannan gyaran haraji yana cikin babban shirin gwamnatinsa da ke neman kyautata yanayin kasuwanci, ƙara samun kuɗaɗen shiga, da kuma ganin ci gaba ya waanzu a faɗin ƙasar.
Yanzu da aka sa ranar fara amfani da dokokin a Janairun 2026, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki suna da lokaci don shirya duk abin da ya kamata domin tabbatar da cewa sabbin dokokin harajin sun cika burinsu na kawo ci gaba ga ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp