Ya kuma yi watsi da ikirarin da ake yi na cewa ‘yansanda na taimakawa wajen magudin zabe, yana mai bayyana irin wadannan zarge-zarge a matsayin mara tushe, tare da cewa aikin ‘yansanda a lokacin zabe ya takaita ne kawai wajen samar da tsaro da tabbatar da zaman lafiya.

“Mu ba ’yan bangar siyasa ba ne, mu kamar alkalan wasa ne, aikin ‘yansanda ya takaita ne kuma ya ta’allaka ga samar da tsaro a lokacin zabe, gwargwadon yadda ya kamata, ba za mu yi zabe ba, jama’a ne za su kada kuri’a, INEC ta kidaya, muna sa ido.

“Kuma wannan ita ce matsayarmu, sannan kuma hanyar da za a bi domin cimma nasara ita ce, sake sabunta hadin gwiwa tsakanin hukumomi, da suka hada da gwamnatin jiha, INEC, da kungiyoyin farar hula, gami da horas da jami’ai domin tabbatar da sun ci gaba da aikinsu yadda ya dace,” in ji shi.

A nasa bangaren, SGF Akume ya ce sauye-sauyen da gwamnatin shugaban Kasa Bola Tinubu ta bullo da su na shimfida ginshikin dorewar zaman lafiyar kasa da kuma bunkasar tattalin arzikin kasa abin a yaba ne.

Akume wanda babban sakataren harkokin siyasa da tattalin arziki a ofishin SGF, Nadungu Gagare ya wakilta, ya ce dole ne sake duba tsakiyar wa’adi inda zai zama aiki ne na tabbatar da dimokuradiyya, ba al’amuran biki ba.

SGF ta lura cewa Tinubu ya karbi mulki ne a daidai lokacin da tattalin arzikin duniya ya tabarbare da kuma lalacewar kasafin kudi na cikin gida, amma duk da haka a cikin shekaru biyu, gwamnatin ta fara aiwatar da sauye-sauyen tsari a muhimman sassa.

“Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya Cibiyar jijiya ce ta hadin gwiwa tsakanin bangarori daban-daban. A cikin shekaru biyu da suka gabata, mun kara himma wajen daidaita manufofin gwamnati da daidaita su da abubuwan ci gaban kasa; da samar da hadin gwiwa tare da Majalisar Dokoki ta kasa, kungiyoyin farar hula, abokan ci gaba, da gwamnatocin kasa da kasa da kuma tallafa wa tsarin aiwatar da ayyukan ci gaba, ciki har da manyan tsare-tsare da suka hada da tsarin aiwatar da ayyukan ci gaba, ciki har da manyan tsare-tsare da suka hada da tsarin aiwatar da ayyukan ci gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce wakilan ƙasarsa za su gana da na Iran domin ci gaba da tattaunawa kan makaman nukiliyarta a mako mai zuwa.

“Za mu tattauna da Iran a mako mai zuwa, ƙila mu ƙulla yarjejeniya ko kuma akasin haka, ba na ce ba,” in ji shi yayin jawabinsa a taron ƙasashe na ƙungiyar ƙawancen tsaro ta NATO da ake yi a ƙasar Netherlands.

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

“Ba su daɗe da gama yaƙi ba, yanzu za su ci gaba da harkokinsu. Ban damu dole sai na ƙulla wata yarjejeniya da su ba,” a cewarsa.

A jiya Talata ce Trump ya soki Isra’ila da Iran, bayan zargin ƙasashen biyu da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla.

Lamarin na zuwa ne bayan ɓullar rahoton kai wa juna hari daga dukkan ƙasashen biyu, duk da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ’yan sa’o’in da suka gabata.

Trump ya ce ƙasashen sun daɗe suna faɗa da juna, kuma a wannan mataki ana iya cewa ba su ma san abin da suke yi ba.

Ya ce: “Ba abin da muke so ke nan ba, ina tabbatar muku cewa ina fushi da abin da suka aikata.”

Shugaba Trump ne mutum na farko da ya fara sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ilan da Iran, bayan shafe kwana 12 suna kai wa juna hare-hare.

Sai dai Iran ta musanta sanarwar da Trump ya yi cewa ta amince da tsagaita wuta a yaƙinta da Isra’ila, inda ta ce ƙofarta a buɗe take don dakatar da yaƙin, matuƙar Isra’ila ta dakatar da kai mata hari.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ne ya yi wannan jawabi, a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X a wannan Talata, yana mai cewa ya zuwa yanzu babu wata matsaya da suka cimma ta tsayar da wannan yaki, har sai Isra’ila ta fara dakatar da farmakinta a Iran, da ƙarfe 4 agogon Tehran, sannan Iran za ta mayar da wukarta cikin kube.

Tun cikin dare Litinin wayewar gari Talata ne Trump ya yi shelar cewa Isra’ila da Iran sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta na mataki-mataki daga ƙarfe 4:00 agogon GMT ranar Talata, da zummar kawo ƙarshen mummunan tashin hankali da aka shafe kusan makonnin biyu ana yi.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce yarjejeniyar ta nemi “cikakkiyar tsagaita wuta,” inda Iran za ta fara daina aiki [kai hare-hare], sannan Isra’ila za ta daina bayan sa’o’i 12.

Ana sa ran tsagaita wutar zai kasance “ƙarshe a hukumance” ga abin da Trump ya kira “Yaƙin kwanaki 12.”

“Bisa zaton cewa komai zai tafi yadda ya kamata, zan so na taya ƙasashen biyu murna, Isra’ila da Iran, game da kasancewa da ƙarfin hali da bajinta da kuma basirar kawo ƙarshen abin da ya kamata a kira “Yaƙin kwanaki 12,” kamar yadda Trump ya wallafa.

Rikicin ya ɓarke ranar 13 ga watan Yuni ne a lokacin da Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare kan wuraren soji da nukiliya da kuma fararen-hula a Iran ciki har da tashar inganta yuraniyom ta ƙarƙashin ƙasa da ke Fordo.

Tehran ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami kan wurare a Isra’ila, lamarin da ya janyo jerin ramuwar gayya da ya ta ƙasashen biyu suka fara kai hare-hare kan juna kai-tsaye.

Tashin hankali ya ƙaru a lokacin da Amurka ta yi tarayya da Isra’ila wajen kai hare-hare ranar 22 ga watan Yuni, inda ta kai hare-hare kan tashoshin nukiliyar Iran uku lamarin da ya sa makami mai linzamin Iran ya kai hari kan sansanin sojin saman Amurka na Al Udeid da ke ƙasar Qatar.

Trump ya haƙiƙance cewa hare-haren da suka kai sun tarwatsa tashoshin nukiliyar na Iran, tare da cewa jami’an ƙasar ba su iya kwashe wani abu daga tashoshin ba “saboda abubuwa ne masu wuyar kwashewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha