’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
Published: 26th, June 2025 GMT
An harbe wasu mutum biyu da ake zargin ’yan fashi da makami ne a ranar Talata a yayin wani artabu da jami’an tsaro suka yi a unguwar Makera da ke Kakuri a Jihar Kaduna.
Rundunar ta kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin tare da ƙwato tarin makamai da kayayyaki masu daraja da aka sace daga mazauna garin.
A cewar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, lamarin ya fara ne da misalin ƙarfe 3:10 na tsakar dare, inda wasu ’yan bindiga 8 suka kai hari a rukunin gidaje na Estate Gashash da ke Barnawa.
Rahotanni sun bayyana cewa, waɗanda ake zargin ɗauke da bindiga ƙirar gida da kuma wasu muggan makamai, an yi zargin sun yi wa mazauna yankin fashin wayoyin salula da kwamfutar tafi-da-gidanka, da agogunan hannu da na’urorin wasanni da sarƙoƙin masu daraja.
Da aka samu kiran gaggawar, babban jami’in ’yan sanda na Barnawa (DPO), tare da haɗin gwiwar DPO na sashen Kakuri da Sabon Tasha, da kuma jami’an runduna ta 312 na Artillery Regiment Kalapanzi, suka garzaya wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa.
Daga baya an bi sawun waɗanda ake zargin har zuwa hanyar Makera, inda aka yi artabu da muggan makamai.
“A fafatawar ne aka kashe biyu daga cikin ’yan fashi da makami, yayin da aka kama wasu biyu,” in ji DSP Hassan.
Ya ce, ana ci gaba da ƙoƙarin kamo sauran ’yan fashin da suka tsere daga yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yan fashi da makami da ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Benuwe, sun kama mutum biyar da ake zargi da hannu a kisan wasu matasa biyu ’yan asalin Jihar Kano.
Waɗanda aka kashe sun haɗa da Jamilu Ahmad da Barhama Suleiman, kuma an kai musu hari ne cikin daren ranar Litinin a unguwar Agan, kusa da ƙofar shiga Makurdi.
Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata BarauAn yi jana’izarsu a ranar Talata a Babban Masallacin Abuja, inda manyan jami’ai suka halarta, ciki har da Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf.
An birne su a maƙabtar Gudu, inda Ribadu da Gwamna Abba sukatabbatar da an yi musu sutura kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada.
Da yake magana da manema labarai bayan jana’izar, Gwamna Abba ya bayyana kisan da cewa: “Abu ne mai ban takaici, zalunci, kuma ba za mu yafe ba.”
Ya buƙaci Gwamnatin Benuwe da hukumomin tsaro su gaggauta kamo waɗanda suka aikata laifin.
“Wannan babban rashi ne ga Kano da ƙasa baki ɗaya. Dole ne a hukunta masu hannu a wannan aika-aika,” in ji Gwamnan.
A gefe guda kuma, ya buƙaci Gwamnatin Jihar Edo ta hanzarta biyan iyalan mafarautan da aka kashe a harin garin Uromi, inda ya yi kira da a tabbatar da adalci da gaskiya wajen magance rikice-rikicen ƙabilanci.
A nasa ɓangaren, Gwamna Hyacinth Alia na Jihar Benuwe, ya yi Allah-wadai da kisan, inda ya ce abin kunya ne kuma ba za su amince da shi ba.
A wata sanarwa daga mai taimaka masa, Tersoo Kula, ya ce ‘yan sanda sun riga sun kama mutum biyar da ake zargi da hannu a lamarin.
“Mutanen Benuwe sun shahara wajen karamci da zaman lafiya. Ba za mu bari wasu ‘yan ta’adda su ɓata mana suna ba. Waɗanda ke da hannu sai sun fuskanci hukunci,” in ji Gwamna Alia.
Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnatin Kano, tare da tabbatar da cewa za a yi adalci.
Gwamna Alia, ya ce ya tattauna da Gwamna Abba kan lamarin, kuma ya roƙi jama’ar Kano da Benuwe su zauna lafiya.
Muhammad Ibrahim Khalil, ɗan uwan ɗaya daga cikin mamatan, ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da ba za su manta da shi ba.
Ya ce abin baƙin ciki ne ganin irin wannan lamari na faruwa a ƙasar da ke da hukumomin tsaro.
Ya roki Allah Ya gafarta musu.
Kisan Jamilu da Barhama ya faru ne a lokacin da ake fama da tashe-tashen hankula a yankin Arewa Ta Tsakiya.
Kwanaki kaɗan kafin faruwar lamarin, wasu ‘yan ɗaurin aure mutum 13 daga Jihar Kaduna sun rasa rayukansu a garin Mangu da ke Jihar Filato.
Gwamnatin Kano ta roƙi jama’ar ta da su kwantar da hankali, su guji ɗaukar fansa, kuma su bar hukuma ta ɗauki mataki.
A cikin wata sanarwa, Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kare ‘yan Kano a ko’ina suke a faɗin Najeriya.
“Kowane ɗan Najeriya yana da ’yancin yin rayuwa, motsi da aiki a ko’ina a cikin ƙasar nan ba tare da tsoro ba.
“Ka da mu bari ƙiyayya da tashin hankali su zama halayenmu,” in ji Gwamna Abba.