Aminiya:
2025-08-11@12:33:47 GMT

’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna

Published: 26th, June 2025 GMT

An harbe wasu mutum biyu da ake zargin ’yan fashi da makami ne a ranar Talata a yayin wani artabu da jami’an tsaro suka yi a unguwar Makera da ke Kakuri a Jihar Kaduna.

Rundunar ta kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin tare da ƙwato tarin makamai da kayayyaki masu daraja da aka sace daga mazauna garin.

An tallafawa iyalan ’yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja

A cewar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, lamarin ya fara ne da misalin ƙarfe 3:10 na tsakar dare, inda wasu ’yan bindiga 8 suka kai hari a rukunin gidaje na Estate Gashash da ke Barnawa.

Rahotanni sun bayyana cewa, waɗanda ake zargin ɗauke da bindiga ƙirar gida da kuma wasu muggan makamai, an yi zargin sun yi wa mazauna yankin fashin wayoyin salula da kwamfutar tafi-da-gidanka, da agogunan hannu da na’urorin wasanni da sarƙoƙin masu daraja.

Da aka samu kiran gaggawar, babban jami’in ’yan sanda na Barnawa (DPO), tare da haɗin gwiwar DPO na sashen Kakuri da Sabon Tasha, da kuma jami’an runduna ta 312 na Artillery Regiment Kalapanzi, suka garzaya wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa.

Daga baya an bi sawun waɗanda ake zargin har zuwa hanyar Makera, inda aka yi artabu da muggan makamai.

“A fafatawar ne aka kashe biyu daga cikin ’yan fashi da makami, yayin da aka kama wasu biyu,” in ji DSP Hassan.

Ya ce, ana ci gaba da ƙoƙarin kamo sauran ’yan fashin da suka tsere daga yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yan fashi da makami da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya

Wasu manyan motocin dakon sun  yi bindiga a yankin Ɗan Magaji da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.

Ana fargabar mutuwar mutane da dama sakamakon gobarar tankokin man bayan sun yi hastari a safiyar Litinin.

Shaidu sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:30 na safe a kusa da Makarantar Rochas Foundation, kan titin Kaduna–Kano bypass daga Kwangila zuwa Dan Magaji.

Hatsarin ya haɗa da manyan motoci biyu masu ɗauke da man fetur da kuma motoci biyu ƙirar Golf ɗauke da fasinjoji.

A sakamakon haka, tankokin biyu suka yi bindiga, wanda ya tayar da wutar gobara mai ƙarfi tare da hayaƙi mai kauri ya lulluɓe hanyar.

Jami’an ceto da tsaro sun rufe hanyar, tare da gargaɗin direbobi da su guji bi ta wurin yayin da ake ci gaba da aikin ceto da dawo da gawarwaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno
  • Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu
  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe