’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
Published: 26th, June 2025 GMT
An harbe wasu mutum biyu da ake zargin ’yan fashi da makami ne a ranar Talata a yayin wani artabu da jami’an tsaro suka yi a unguwar Makera da ke Kakuri a Jihar Kaduna.
Rundunar ta kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin tare da ƙwato tarin makamai da kayayyaki masu daraja da aka sace daga mazauna garin.
A cewar kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, lamarin ya fara ne da misalin ƙarfe 3:10 na tsakar dare, inda wasu ’yan bindiga 8 suka kai hari a rukunin gidaje na Estate Gashash da ke Barnawa.
Rahotanni sun bayyana cewa, waɗanda ake zargin ɗauke da bindiga ƙirar gida da kuma wasu muggan makamai, an yi zargin sun yi wa mazauna yankin fashin wayoyin salula da kwamfutar tafi-da-gidanka, da agogunan hannu da na’urorin wasanni da sarƙoƙin masu daraja.
Da aka samu kiran gaggawar, babban jami’in ’yan sanda na Barnawa (DPO), tare da haɗin gwiwar DPO na sashen Kakuri da Sabon Tasha, da kuma jami’an runduna ta 312 na Artillery Regiment Kalapanzi, suka garzaya wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa.
Daga baya an bi sawun waɗanda ake zargin har zuwa hanyar Makera, inda aka yi artabu da muggan makamai.
“A fafatawar ne aka kashe biyu daga cikin ’yan fashi da makami, yayin da aka kama wasu biyu,” in ji DSP Hassan.
Ya ce, ana ci gaba da ƙoƙarin kamo sauran ’yan fashin da suka tsere daga yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yan fashi da makami da ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Tankokin mai sun yi bindiga a Zariya
Wasu manyan motocin dakon sun yi bindiga a yankin Ɗan Magaji da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.
Ana fargabar mutuwar mutane da dama sakamakon gobarar tankokin man bayan sun yi hastari a safiyar Litinin.
Shaidu sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:30 na safe a kusa da Makarantar Rochas Foundation, kan titin Kaduna–Kano bypass daga Kwangila zuwa Dan Magaji.
Hatsarin ya haɗa da manyan motoci biyu masu ɗauke da man fetur da kuma motoci biyu ƙirar Golf ɗauke da fasinjoji.
A sakamakon haka, tankokin biyu suka yi bindiga, wanda ya tayar da wutar gobara mai ƙarfi tare da hayaƙi mai kauri ya lulluɓe hanyar.
Jami’an ceto da tsaro sun rufe hanyar, tare da gargaɗin direbobi da su guji bi ta wurin yayin da ake ci gaba da aikin ceto da dawo da gawarwaki.