Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Published: 27th, June 2025 GMT
Kwanan baya, jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Cing-te, ya fitar da wani bayani a fili, inda a ciki ya canja asalin tarihin kasar Sin, kana ya musanta cewa yankin Taiwan wani yanki ne na kasar Sin tun da da can, kuma, ya kauce wa yin tsokaci kan jerin takardun dokoki na kasashen duniya, wadanda suka bayyana yankin Taiwan a matsayin wani yanki na kasar Sin bayan yakin duniya na biyu.
Kazalika, ya kalubalanci kuduri mai lamba 2758 na babban taron MDD da dokokin kasashen duniya. Babu shakka, abin da Lai Cing-te ya yi ya sa ya zama abokin gaban dukkan al’ummomin kasar Sin, da yawansu ya zarce biliyan 1 da miliyan 400, kana ya mai da shi kansa a matsayin mai adawa da tsarin kasa da kasa da yanayin adalci na duniya.
Sai dai, ko me mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te za su yi, ba zai canja anihin batun ba, wato yankin Taiwan wani yanki ne na kasar Sin, kuma ba zai canja ra’ayin gamayyar kasa da kasa ba na tsayawa tsayin daka kan manufar “kasar Sin kasa daya tak” a duniya, balle hana dunkulewar kasar Sin baki daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yankin Taiwan na kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
A yau Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Mozambique Daniel Francisco Chapo, suka mikawa juna sakon taya murnar cika shekaru 50 da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.
A cikin sakonsa, shugaba Xi ya bayyana fatansa na kara hadin gwiwa da Chapo, a fannin yayata dadadden zumuncinsu bisa wannan zarafi mai kyau, da kuma zurfafa hadin gwiwarsu bisa tabbatar da ingantacciyar shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kuma dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka da sauransu.
A nasa bangare, Chapo ya ce, kasarsa na fatan zurfafa huldar bangarorin biyu, bisa tushen mutunta juna, da samun ci gaba da cin moriya tare, da kuma habaka hadin kai, da kiyaye tsarin gudanar da harkokin kasa da kasa tsakanin mabambantan bangarori. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp