Aminiya:
2025-11-08@17:19:42 GMT

Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara

Published: 25th, June 2025 GMT

Daya daga cikin manyan ’yan bindigar da suka addabi Najeriya, Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a wani harin kwanton bauna da ya kai a jihar Zamfara ranar Lahadi.

Bayanai sun nuna daga cikin wadanda aka kashe din har da wasu jami’an hukumar tsaro ta DSS su hudu da kuma wani tubabben dan bindiga da yanzu yake aikin bayar da bayanai ga jami’an tsaro, Bashar Maniya.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa an kai harin ne a kusa da Rugar Chida, wani kauyen da mahaifin Bello Turjin ke rike da sarautar gargajiya.

Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027 An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya

An dai yi wa jami’an da ke tafiya a cikin motoci biyu da babura kwanton baunar ne a yankin wanda ya shafe mako biyu babu sabis din waya saboda aikin da sojoji suke a ciki.

Wata majiya a yankin ta tabbatar wa Aminiya cewa harin ya daga musu hankali matuka kuma an shirya shi yadda ya kamata.

Majiyar ta ce, “An mamaye su. Bello Turji da yaransa sun kashe mutum 40 daga cikinsu sannan suka kwace ababen hawan da suke kai.

“Turji ya ji dadin harin sosai musamman saboda Bashar Maniya na cikin wadanda aka kashe, wanda tun a baya dama babban abokin hamayyarsa ne kafin ya tuba daga ta’addancin,” in ji majiyar.

A cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an ga Bello Turji yana murna tare da nuna gawarwakin mutanen, ciki har da ta Bashar Maniya, yana rera wakokin cin nasara.

“Wannan ce gawar Kwamandan da ya jagoranci harin,” kamar yadda aka jiyo Turjin yana bayyanawa a cikin bidiyon.

Daga bisani dai an kwaso gawarwakin mutanen tare da gudunmawar sojojin sama, yayin da wadanda suka jikkata kuma aka garzaya da su asibiti.

Wani jami’in tsaro da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi da abin takaici da za a iya kauce masa matukar ana aiki tare tsakanin jami’an tsaro da mutanen gari.

Bayanai dai sun nuna gabanin kisan mayakan, an kashe ’yan bindiga yaran Bello Turji sama da 30 a wata ba-ta-kashi da aka yi tsakanin yaran Turjin da na Maniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan sa Kai Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na shiyyar Abuja (AEDC) ya fara aikin rage ma’aikata kusan 800, a daidai lokacin da ’yan Najeriya ke ci gaba da fama da hauhawar farashi, tsadar rayuwa, da rashin tabbas wajen samun wutar lantarki.

Matakin korar wanda ta fara a ranar Laraba, ya biyo bayan watanni na sake fasalin cikin gida a kamfanin da ke ba da wutar lantarki ga Babban Birnin Tarayya Abuja da jihohin Kogi, Neja da Nasarawa.

Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah

Majiyoyi da dama da ke da masaniya kan lamarin sun shaida cewa shugabannin kamfanin sun fara ne da shirin korar ma’aikata 1,800, kafin su rage adadin zuwa 800 bayan jerin tattaunawa masu zafi da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Ƙasa da Ƙungiyar Ma’aikatan Wutar Lantarki da Ƙungiyoyin Kwadago.

Wata majiya daga cikin ma’aikatan AEDC ta ce shugabannin kamfanin sun fara da shirin korar 1,800, amma sun rage zuwa 800 bayan matsin lamba daga ƙungiyoyin, waɗanda a farko suka dage cewa ba a kamata a kori kowa ba.

“Shugabanni sun so su kori 1,800, amma bayan matsin lamba, sun rage zuwa 800. Tun da farko kungiyoyin sun nemi kada a kori kowa,” in ji ma’aikacin da ya nemi a boye sunansa don kauce wa hukunta shi.

“Ƙungiyoyin sun fara da cewa kada a kori kowa, amma daga baya an ce sun amince da 800. Ma’aikatan da abin ya shafa sun kamata su fara karɓar takardunsu daga ranar Litinin, amma an jinkirta, sai jiya aka fara ba su takarda,” wata majiya ta bayyana.

Wata takardar sallama mai taken “Sanarwar Sallama Daga Aiki”, da aka rubuta a ranar 5 ga Nuwamba, 2025, kuma Adeniyi Adejola, Babban Jami’in Kula da Ma’aikata na kamfanin, ya sanya wa hannu, ta tabbatar da cewa aikin na daga cikin “shirin daidaita ma’aikata da ake ci gaba da aiwatarwa.”

Takardar ta kuma bayyana cewa duk ma’aikatan da abin ya shafa za su karɓi haƙƙinsu bayan kammala tsarin sallamar su.

Wani ɓangare na takardar ya ce: “Muna bakin cikin sanar da kai cewa ba za a sake buƙatar ayyukanka a kamfanin nan ba daga ranar 5 ga watan Nuwamba, 2025. Wannan shawara ta biyo bayan sakamakon aikin daidaita ma’aikata da kamfanin ke aiwatarwa. Ka tabbata cewa an yanke wannan shawara bayan dogon nazari da kuma bisa ka’idojin kamfanin.”

“Ana buƙatar ka kammala tsarin sallama a wurin aikinka, ka kuma dawo da duk wani kayan kamfani da ke hannunka kafin ka mika kanka ga wakilin kula da ma’aikata. Kammala waɗannan matakai ne zai ba da damar sarrafa kuɗin sallamarka,” in ji takardar sallamar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140