Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Published: 26th, June 2025 GMT
Yawan gawarwakin da aka tsinta bayan harin duk na mabiyansa ne.
Ɗaya daga cikin su, Bashari Maniya, wanda tsohon ɗan bindiga ne da ya ce ya tuba kuma ya fara taimaka wa jami’an tsaro, shi ma ya mutu bayan motar da yake ciki ta faɗa rami mai zurfi.
Manga ya bayyana cewa ba da bindiga aka kashe Maniya ba, saɓanin jita-jitar da ke yawo.
“Sabuwar mota ce, kuma ba su san dajin sosai ba. Yayin da suke gudu a cikin daji, sai suka faɗa cikin wani rami mai zurfi. Motar ta kife, kuma an kasa ciro ta cikin sauƙi,” in ji shi.
Ya ce lokacin da aka zo taimaka musu, an same su a cikin motar a sume. Motar ba ta da kariyar harsashi, amma hatsarin ya jikkata su sosai.
Mai ba da shawarar ya ƙara da cewa Gwamna Dauda Lawal yana da cikakken goyon bayan ganin an kamo Bello Turji.
“Ba za mu haƙura ba sai mun murƙushe Turji. Mutanen Zamfara, musamman ma a Shinkafi, sun san irin azabar da ya jefa su ciki fiye da shekaru 14 da suka wuce,” in ji shi.
Manga ya ce gwamnati na shirin ƙara tura sojoji domin ƙarfafa yaƙi da ƙungiyar Turji da sauran ’yan ta’adda a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Hari Jami an Tsaro Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta samu nasarar ceto mutum 10 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su tsawon watanni huɗu da suka gabata a Ƙaramar Hukumar Kagarko.
A cikin sanarwar da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka ceto har da yara masu shekaru ɗaya, uku da kuma 13.
Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaroDSP Mansir, ya ce ’yan bindigar sun kai farmaki ƙauyen Kushe Makaranta, inda suka sace mutanen daga gidajensu sannan suka kai su dajin da ke kusa da Rijana.
Rundunar, ta ce aikin ceto mutanen ya samu ne ta haɗin gwiwar ’yan sanda, jami’an DSS, da kuma sojoji.
Wani mazaunin yankin ya shaida cewa suna matuƙar farin ciki da wannan nasara, musamman ganin cewa mutanen sun kwashe watanni a hannun ’yan bindiga cikin tsananin wahala.
Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike domin kamo sauran ‘yan bindigar da suka tsere, tare da inganta matakan tsaro a yankin don kauce wa sake faruwar irin wannan lamarin.
“Za mu ci gaba da aiki tare da sauran hukumomi don tabbatar da cewa babu wata ƙungiyar ‘yan ta’adda da za ta samu mafaka a Kaduna,” in ji DSP Mansir Hassan.