Aminiya:
2025-11-27@21:54:54 GMT

Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici

Published: 26th, June 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Neja, ta rufe Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU) da ke Lapai saboda matsalolin tsaro da suka janyo mutuwar wasu ɗalibai.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Abubakar Usman, ya ce an ɗauki wannan matakin ne saboda rashin tabbacin tsaro da ke barazana ga rayuwar ɗalibai da ma’aikata.

Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum 1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Gwamna Umaru Bago ya amince da rufe jami’ar nan take, kuma za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu sauyi.

“Lafiyar kowa, musamman ɗalibai da malamai, na da matuƙar muhimmanci ga gwamnatin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da abin da ya faru, kuma muna ɗaukar matakan gaggawa don magance lamarin.”

Gwamnatin ta roƙi ɗalibai, malamai da ma’aikatan jami’ar su kwantar da hankalinsu, kuma su kasance masu lura, su kuma yi aiki tare da jami’an tsaro a wannan lokaci.

Haka kuma gwamnatin ta tabbatar da cewa tana ɗaukar matakai domin wanzar da zaman lafiya.

Ta ce duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

“Za mu ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da kuma tabbatar da doka da oda a faɗin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gwamnatin Neja

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi

An ceto ’yan matan nan 24 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Makarantar sakandaren Gwamnati ta GGCSS da ke yankin Maga da ke Jihar Kebbi.

Gwamnan jihar Kebbi Nasiru Idiris a taron manema labarai a ranar Talata fadar gwamnatin jihar ya tabbatar da an karɓo ɗalibban da aka sace a farkon makon nan.

Ya ce “an karɓo ɗiyanmu ’yan makaranta waɗanda aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya baiwa jami’an tsaro umarni a tafi a gano inda yaran suke kuma a karɓo su muna tabbatar wa uwayen yara da al’ummar Kebbi yara sun dawo.

“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro musamman sojoji da ’yan sanda da Sibil difens da sauransu da suka tsaya aka karɓo yaran nan cikin ƙoshin lafiya.

“Mu gwamnatin Kebbi ba mu biya kuɗin fansa don a saki yaran ba, a binciken da muka yi ba wanda ya biya kuɗin fansar yaran, mu ba mu ba da ko kwabo ba,” a cewar Gwamnan Idiris.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja