Leadership News Hausa:
2025-12-14@09:42:22 GMT

Wata Miyar Sai A Makwabta…

Published: 13th, March 2025 GMT

Wata Miyar Sai A Makwabta…

Idan ka dauki bangaren tsofaffi da kananan yara, za ka iya cewa su ne mafi rauni a cikin al’umma. Tsofaffi sun gajiya don haka suna bukatar taimako, yara kanana kuma ba su kawo karfi ba, bisa haka dole suna bukatar madafa. A nan, sai mu ce gwamnatin Sin ta yi tunani mai kyau.

Kundin rahoton ya kuma bayyana cewa, a shekarar 2025 gwamnatin kasar za ta kara zage damtse wajen raya kauyukan dake rabe da birane da gyara gine-ginen da suka tsufa.

Ga duk wanda yake shiga yankunan kauyuka da ke cikin birane (kamar unguwannin masu karamin karfi) ko wadanda suke rabe da su zai ga ba su da kyawun gani, domin kayayyakin alatu da kayatattun gine-gine da ababen more rayuwa da ake samarwa a cikin birane ba za su taba bari taurarin wadannan kauyuka su haska ba. Domin tabbatar da ci gaba da zamanintar da kasar Sin yadda ya kamata, dole ne a tafi tare da ire-iren wadannan kauyuka cikin ayyukan ci gaba da ake gudanarwa.

Har ila yau, rahoton ayyukan gwamnatin ya bayyana cewa, a bana, gwamnatin kasar ta kudiri aniyar kara yawan kudin tallafin muhimman ayyukan inshorar kiwon lafiya ga mazauna karkara da marasa aikin yi na birane, inda aka kara yawan kudin da yuan 30 ga kowane mutum. Ko tantama babu, tabbas wannan zai kara inganta kiwon lafiyar al’umma musamman marasa karfi.

Bugu da kari, tallafin kiwon lafiyar bai tsaya nan ba, akwai wani kaso na musamman da gwamnatin za ta ware na tallafin kudin kiwon lafiya ga daukacin al’umma a bangaren muhimman bukatunsu inda shi ma aka kara yawansa da yuan 5 ga kowane mahaluki da zai ci gajiya.

Baya ga batun tallafi na zuwa asibiti, gwamnatin ta kuma yi wata farar dabara da za ta kara inganta koshin lafiya ta hanyar sanya gina dandaloli da dakunan wasannin motsa jiki a kusa da gidajen al’umma a cikin kundin rahoton ayyukanta na 2025. Wannan dabara za ta kara inganta kiwon lafiyar al’umma saboda kowa ya san yadda motsa jiki ya zama wajibi ga duk wanda yake son samun koshin lafiya.

Kazalika, da yake zamani na ci gaba da sauyawa ta fuskar komai da komai, gwamnatin kasar Sin ta sha alwashin hanzarta komawa amfani da tsarin biyan kudade na zamani da aka inganta domin kara saukaka hada-hada da harkokin kudade.

Duka wadannan abubuwa an bullo da su ne domin cimma muradun jama’a da kara kula da bukatunsu. A gaskiya ina kwadayin ganin irin wannan tsari a kasashenmu na Afirka, saboda muhimmanta bukatun jama’a alhaki ne da ke rataye a wuyar gwamnati. Ya kamata shugabanninmu su sa himma da kwazo don su raba mu da tunanin “wata miyar sai a makwabta”, a duk lokacin da muka ga yadda ake kula da muradun al’umma a wasu kasashe, musamman kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC

Jam’iyyar ADC ta zargi Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC) da amfani da siyasa wajen belin tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami (SAN).

Jam’iyyar ta ce babu wata shaida da ke nuna cewa Malami ya karya sharuɗan belin da aka ba shi.

Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce an ɗauki matakin ne jim kaɗan bayan Malami ya halarci wani taron siyasa a Jihar Kebbi.

Jam’iyyar ta ce matakin da aka ɗauka ya nuna yadda aka ƙulla wani abu domin daƙile burinsa na takarar gwamna, ba wai domin neman adalci ba.

“Jam’iyyar ADC na kallon soke belin Malam Abubakar Malami da EFCC ta yi a matsayin amfani da siyasa,” in ji Abdullahi.

“Daga dukkanin bayanan da muka samu, Malami bai karya ko ɗaya daga cikin sharuɗan belin da aka ba shi ba, kuma hana belin ya sanya alamar tambaya a kan manufar EFCC.”

ADC ta ce tana goyon bayan yaƙi da cin hanci da rashawa tare da mara wa EFCC baya wajen gudanar da aikinta.

Sai dai jam’iyyar ta yi gargaɗin cewa ɗaukar matakai na ɓangare ɗaya kan ‘yan adawa na iya rage amincewar jama’a da kuma raunana sahihancin yaƙi da cin hanci a ƙasar.

Jam’iyyar ta kuma ce babu wata hukuma ta gwamnati da ke da ikon hana ɗan ƙasa shiga harkokin siyasa ba tare da umarnin kotu ba.

Ta ƙara da cewa tana tare da Malami, tare da yin kira da a sake nan take ba tare da sharuɗan da za su taƙaita masa haƙƙinsa na siyasa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau
  • EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC
  • Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya
  • Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa