Leadership News Hausa:
2025-08-11@02:09:05 GMT

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Published: 26th, June 2025 GMT

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

 

Bello, a wata sanarwa da ya fitar ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Muawiyah Yusuf, ya bayyana matukar bacin ransa da alhininsa kan wannan mummunan harin.

 

Sanata Bello wanda kuma tsohon gwamnan jihar Neja ne, ya yi jinjina ga sojojin da suka rasa rayukansu a bakin aiki, inda ya bayyana su a matsayin jarumai na kasa wadanda suka sadaukar da rayuwarsu domin kare zaman lafiya da ‘yancin Nijeriya.

 

Ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan sojojin da suka rasu, yana mai addu’ar Allah ya kara musu lafiya, ya basu hakurin juriya da irin wannan rashi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Inganta Fannin Lafiya Da Sauran Ababen More Rayuwa A Sule Tankarkar

Majalisar zartarwa ta karamar hukumar Sule Tankarkar dake Jihar Jigawa ta amince da gudanar da muhimman ayyuka a bangarorin kiwon lafiya da sauran aikace-aikacen ci gaban al’umma.

 

Taron majalissar bisa jagorancin shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Tasi’u Adamu, ya kuma amince da gina makarantun Tsangaya guda 3 na zamani da za’a sanyawa sunayen wasu fitattun yan siyasa na yankin da suka rasu.

 

Yayi bayanin cewar, za’a gina makarantun tsangayar ne a garuruwan Danzomo da Shabaru da kuma Rukutu wadanda za’a sanyawa sunan wadanda suka rasu da suka hada da marigayi Sanata Dalha Ahmad Dan Zomo da marigayi Musa Waziri Kamus da kuma marigayi Ali Ado.

 

Haka kuma majalisar ta amince da gyaran masallatan Juma’a na Hannun Giwa da Dan Ladin Gumel da masallacin Tsangaya na Sule Tankarkar.

 

Alhaji Tasi’u yace za’a gina sabbin masallatan kamsisalawati guda 5 a garuruwan Chiromawa da Kofar Yamma da kuma Babban Sara.

 

Majalissar ta kuma amince da gina asibitoci matsakaita guda 3 a Dan Makama da Mabia da kuma Sarkin Gandu.

 

Shugaban karamar hukumar yace za’a gina magudanan ruwa da kuma samar da ruwan sha mai amfani da hasken rana a garin Lula.

 

Har il! yau Majalisar zartarwar ta kuma amince da sayo kayayyakin gyaran tuka tuka na naira miliyan 11 da kuma amincewa da naira miliyan 5 da dubu dari 5 domin sayen magunguna da feshin maganin sauro.

 

Kazalika, an amince da gyaran ofishin shugaban majalissar kansiloli da kuma ofisoshin masu bada shawara guda 7 don inganta ayyukan gwamnati a yankin.

 

Tasi’u, yace ayyukan na daga cikin kudirorin sa guda 5 da yayi koyi da ga cikin kudirorin Gwamna 12 domin kyautata rayuwar jama’ar yankin.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno
  • Za A Inganta Fannin Lafiya Da Sauran Ababen More Rayuwa A Sule Tankarkar
  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano
  • Jirgin Daukar Marasa Lafiya Ya fadi A kasar kenya Ya Kuma Kashe Akalla mutane 6