Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
Published: 26th, June 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe ta amince da fitar da Naira biliyan 6.563 kuɗin giratuti domin biyan haƙƙoƙin ’yan fansho da suka yi ritaya daga shekarar 2021 zuwa 2023.
Wannan sanarwar ta fito ne bayan taron Majalisar Zartarwa karo na 48 wanda Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya jagoranta.
Arsenal za ta ɗauki ɗan ƙwallon Brentford Christian Norgaard Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — TrumpKwamishinan Kuɗi da Tattalin Arziki, Muhammad Gambo Magaji, ya bayyana cewa Naira biliyan 1.
Sannan kuma za a biya Naira biliyan 2.342 a watan Disamba ga waɗanda suka yi ritaya a shekarar 2023, kamar yadda kwamishinan ya bayyana.
Da wannan mataki dai gwamnatin za ta cike gibin bashin kuɗin giratuti da Gwamnatin Inuwa Yahaya ta gada, wanda ya kai sama da Naira biliyan 21 a shekarar 2019.
“Zuwa yanzu, an riga an biya sama da Naira biliyan 17, wanda ke nuna jajircewar gwamnatin wajen kula da jin daɗin ma’aikata.”
Da wannan biyan na baya-bayan nan, gwamnatin na gab da kammala biyan dukkan hakkokin giratuti daga shekarar 2014 zuwa 2023, wanda ke tabbatar da alkawarin ta ga wadanda suka yi ritaya tare da dawo da amana tsakanin gwamnati da al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Giratuti jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahaya da suka yi ritaya Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
A cewar ‘yansanda, “A ranar 10/10/25, an gayyato wani Mista Oke Emmanuel, dan NYSC kuma abokin dakin wanda ya bace, domin yi masa tambayoyi. Ya tabbatar cewa wanda ake nema ya kasance tare da iyalan George har zuwa 06/10/25.
“An samu karin bayani daga George cewa dan NYSC din ya koka da rashin lafiya, aka kai su Asibitin Kaiama Referral Hospital a ranar 04/10/25, kuma aka sallame shi ranar 05/10/25. Sai dai a ranar 06/10/25, dan NYSC din ya bace zuwa wani wurin da ba a sani ba.”
‘Yansanda kuma suna binciken zargin karbar kudin rashawa na Naira 100,000 daga iyayen wanda ya bace, da wasu fursunoni biyu da ke gidan gyaran hali na Igbara, Abeokuta, Jihar Ogun, wadanda suka yi suna kamar masu garkuwa da mutane.
“An bar wayar salula ta wanda ya bace a dakinsa. Jami’an bincike suka bi layin kira daga lambar 0906193291, inda aka gano tana hannun wani fursuna da ake tsare da shi a cibiyar gyaran hali ta Igbara, Abeokuta, saboda wani laifin garkuwa da mutane.
“Wanda ake zargin ya ce sun ga lambar wayar a kafafen sada zumunta, suka yi amfani da ita don cutar da mahaifin wanda ya bace, Mista Anyanwu Simon, mai shekara 56. An biya kudin Naira 100,000 zuwa asusun Opay mai lamba 7042793493 na wata Atinuke Oluwalose, abokiyar hadin bakin fursunan da ke gidan yarin Abeokuta.”
“Daga bayanan da jami’an bincike suka gano, akwai wasu abubuwan damuwa da ka iya kasancewa silar abin da ya faru. An gano wasu kalaman da wanda ya bace ya yi dangane da wasu sabbin dabi’u da sha’awowi da ba su dace da akidar addininsa ba,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta kammala da cewa ana ci gaba da daukar matakan bincike “domin tabbatar da sakamakon da jami’an bincike suka tattara, kasancewar binciken ya fito da abubuwa masu ban mamaki. Ba a samu wata alamar garkuwa da mutane a wannan lamari ba. Ana ci gaba da aiki domin samun cikakken bincike.”
PUNCH Metro ta ruwaito a watan Oktoba 2024 cewa an kama mutum hudu kan bacewar wani dan NYSC mai suna Yahya Faruk, wanda yake hidima a Ikuru, cikin Karamar Hukumar Andoni ta jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA