Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne?
Published: 28th, February 2025 GMT
A ranar Litinin ne Jam’iyyar NNPP ɓangaren Kwankwasiyya a Kano, ta fitar da sanarwar dakatar da jiga-jigan ’yan siyasarta huɗu.
An dakatar da Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, da sauran ’yan majalisar wakilai uku, da suka haɗa da Aliyu Sani Madakin Gini da Kabiru Alhassan Rurum da kuma Abdullahi Sani Rogo.
Sai dai ba kowa ne ya san asalin mafarin rigimar ’yan majalisar da madugunnKwankwasiyyam Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ba.
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli.
Yadda kasuwar buƙata ta haɗe su da Kwankwaso a 2023
Dama dai ana ganin Sani Rogo da Kawu Sumaila, asali ba su da gami da tafiyar siyasar Kwankwasiyya, amma saboda kasuwar buƙata ce, suka haɗe daga baya.
Abdullahi Sani Dogo ya koma jikin Kwankwaso ne tun bayan raba gari da tafiyar gidan Malam Ibrahim Shekarau.
Shi kuma Kawu Sumaila, ya koma jikin Kwankwaso ne gab da zaɓen 2023.
Kabiru Alasan Rurum, asali ɗan Kwankwasiyya ne, amma ya bart a a lokacin Gwamnatin Ganduje, har ya zama Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano. Sai dai bayan hana shi takarar gwamna a Jam’iyyar APC, ya koma gidansa na da, wato Kwankwasiyya.
Wanda aka fi yin mamakin saɓaninsa da tsarin Kwankwasiyya shi ne Ali Sani Madakin Gini, ganin yadda a zamanin Ganduje, ya rasa kujerar ɗan Majalisar Tarayya saboda nuna biyayya ga Kwankwaso.
Ainihin tushen saɓaninsu da Kwankwaso
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso da kansa ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli, ba tare da bai wa ɗaya da cikin waɗannan jiga-jigai dama ba.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa, babu wanda aka bai wa dama a cikinsu a fitar da shugabancin ƙananan hukumomin da suka fito, abin da suke ganin tamkar cin fuska ne ga buwayarsu ta siyasa.
Misali da ƙaramar hukumar Sumaila, a yadda aka saba, Kawu Sumaila shi yake kafa shugabanci a matakin ƙaramar hukumar, amma a wannan karon, Kwankwaso ya bai wa Faruk Abdu, ɗan tafiyarsa na asali, wanda kuma bai cika shiri da Kawu Sumaila ba a siyasance.
Tun daga lokacin ake zaman doya da manja, har ake zargin ’yan majalisar da ƙara rura wuta a tafiyar Abba Tsaya da Kafarka da ta kunno kai a kwanakin baya.
Makomar siyasar Kwankwasiyya
A yanzu haka, ’yan majalisar da aka dakatar sun barranta kansu da NNPP mai littafi, inda suka bayyana cewa, su ’yan Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ne. Kuma a yanzu haka maganar tana kotu, kan wane ɓangare ne ke da halaccin a matsayin jam’iyya.
’Yan Kwankwasiyya a Kano na kallon ’yan majalisar huɗu a matsayin masu butulci. Misali da Kawu Sumaila da ya daɗe yana neman Sanata bai samu ba, har sai da ya haɗa tafiya tare da Kwankwaso.
Ana ganin Kwankwasiyya ka iya samun rauni, musamman a Kano ta Kudu, idan har aka tafi a haka. Kuma da ma tun a zaɓen 2023, Kwankwasiyya ba ta da ƙarfin a-zo-a-gani a yankin Kano ta Arewa.
Abun jira a gani shi ne ko Kwankwaso zai yafe wa ’yan majalisar, a tunkari zaɓen 2027 tare, tun da dai siyasa kasuwar buƙata ce.
Ko kuma zai zaɓi zama shi ƙadai gayya a zaɓe mai zuwa, kamar yadda ya sha gwadawa a baya tana kai masa.
Idan ko hakan ya zaɓa, tabbas za a doka siyasa, kuma a cikin biyu a yi ɗaya: Walau ya koya musu darasinta, ko kuma su nuna masa ƙarfinsu ya kawo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kawu Sumaila Kwankwasiyya Kwankwaso Siyasa yan majalisar Kawu Sumaila da Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano
Gwamnatin Kano ta sanar da cewa akwai aƙalla fiye da mutum miliyan 1.2 da ke fama da ciwon hanta da ake kira Hepatitis B a faɗin jihar.
Kwamishinan Lafiya, Dokta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yau Litinin yayin wani taron manema labarai a Cibiyar Tiyata ta Gaggawa da ke Asibitin Nasarawa a birnin Dabo.
Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000 An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a NejaAminiya ta ruwaito cewa wannan sanarwar na zuwa ne a daidai Ranar Ciwon Hanta ta Duniya ta bana.
Kwamishinan ya bayyana ciwon hanta a matsayin matsala babba da ana iya magance ta matuƙar an miƙe tsaye a kai.
Ya yi bayanin cewa muddin ba a farga ba ko kuma aka yi sakaci, cutar tana iya shafar ƙoda ko ma ta rikiɗe zuwa ciwon daji.
Dokta Labaran ya sanar da cewa Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan domin tallafa wa ƙoƙarin da take yi na aiwatar da shirin daƙile yaɗuwar ciwon hantar a tsakanin mata da jaririnsu da ake kira “HepFree UwadaJariri”— wanda aka ƙaddamar tun a watan Fabrairun bana.
Kano ita ce jihar ta farko a Nijeriya da ta ƙaddamar tare da ware kuɗi domin shirin nan na daƙile ciwon hanta ta hanyar duba lafiya da kuma bai wa mata masu juna biyu magani kyauta waɗanda aka gano suna ɗauke da cutar.
Kwamishinan ya ce ana gudanar da wannan aiki a manyan cibiyoyin lafiya bakwai da suka haɗa da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, da Asibiti Ƙwararru na Murtala Muhammad, da Asibitin Koyarwa na Abdullahi Wase, da manyan Asibitoci da ke garin Bichi, da Gaya, da kuma Wudil.
Yau ce ranar yaƙi da cutar ciwon hanta ta duniya wadda ta yi daidai da 28 ga watan Yuli.
Hukumar Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce mutane da dama ne ke ɗauke da wannan cuta wadda a Turance ake kira Hepatitis, amma ba tare da sun sani ba.
Alƙaluma sun nuna cewa, miliyoyin mutane ne cutar ta Hepatitis ke hallakawa a faɗin duniya.
An dai ware wannan rana ne domin jawo hankali ga illar wannan cutar, da kuma hanyoyin da ya kamata a bi domin shawo kanta.
Likitoci na shawartar al’umma da su riƙa zuwa gwajin cutar domin ba kasafai take nuna alamu ba kafin ta yi tsanani.
Shi dai ciwon hanta ko kuma Hepatitis na da nau’i kashi biyar da suka haɗa da:
Ciwon hanta ajin A
Ciwon hanta ajin B
Ciwon hanta ajin C
Ciwon hanta ajin D
Ciwon hanta ajin E
Sai dai ƙwararru sun ce nau’in da suka fi illa da haɗari su ne ajin A da na B wata Hepatitis A da Hepatitis B.
Shi ciwon hanta ajin B wato Hepatitis B yana da rigakafi. Amma Hepatitis C ba shi da rigakafi amma kuma maganinta na warkarwa ɗari bisa ɗari, a cewar ƙwararru.