Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne?
Published: 28th, February 2025 GMT
A ranar Litinin ne Jam’iyyar NNPP ɓangaren Kwankwasiyya a Kano, ta fitar da sanarwar dakatar da jiga-jigan ’yan siyasarta huɗu.
An dakatar da Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, da sauran ’yan majalisar wakilai uku, da suka haɗa da Aliyu Sani Madakin Gini da Kabiru Alhassan Rurum da kuma Abdullahi Sani Rogo.
Sai dai ba kowa ne ya san asalin mafarin rigimar ’yan majalisar da madugunnKwankwasiyyam Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ba.
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli.
Yadda kasuwar buƙata ta haɗe su da Kwankwaso a 2023
Dama dai ana ganin Sani Rogo da Kawu Sumaila, asali ba su da gami da tafiyar siyasar Kwankwasiyya, amma saboda kasuwar buƙata ce, suka haɗe daga baya.
Abdullahi Sani Dogo ya koma jikin Kwankwaso ne tun bayan raba gari da tafiyar gidan Malam Ibrahim Shekarau.
Shi kuma Kawu Sumaila, ya koma jikin Kwankwaso ne gab da zaɓen 2023.
Kabiru Alasan Rurum, asali ɗan Kwankwasiyya ne, amma ya bart a a lokacin Gwamnatin Ganduje, har ya zama Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano. Sai dai bayan hana shi takarar gwamna a Jam’iyyar APC, ya koma gidansa na da, wato Kwankwasiyya.
Wanda aka fi yin mamakin saɓaninsa da tsarin Kwankwasiyya shi ne Ali Sani Madakin Gini, ganin yadda a zamanin Ganduje, ya rasa kujerar ɗan Majalisar Tarayya saboda nuna biyayya ga Kwankwaso.
Ainihin tushen saɓaninsu da Kwankwaso
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso da kansa ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli, ba tare da bai wa ɗaya da cikin waɗannan jiga-jigai dama ba.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa, babu wanda aka bai wa dama a cikinsu a fitar da shugabancin ƙananan hukumomin da suka fito, abin da suke ganin tamkar cin fuska ne ga buwayarsu ta siyasa.
Misali da ƙaramar hukumar Sumaila, a yadda aka saba, Kawu Sumaila shi yake kafa shugabanci a matakin ƙaramar hukumar, amma a wannan karon, Kwankwaso ya bai wa Faruk Abdu, ɗan tafiyarsa na asali, wanda kuma bai cika shiri da Kawu Sumaila ba a siyasance.
Tun daga lokacin ake zaman doya da manja, har ake zargin ’yan majalisar da ƙara rura wuta a tafiyar Abba Tsaya da Kafarka da ta kunno kai a kwanakin baya.
Makomar siyasar Kwankwasiyya
A yanzu haka, ’yan majalisar da aka dakatar sun barranta kansu da NNPP mai littafi, inda suka bayyana cewa, su ’yan Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ne. Kuma a yanzu haka maganar tana kotu, kan wane ɓangare ne ke da halaccin a matsayin jam’iyya.
’Yan Kwankwasiyya a Kano na kallon ’yan majalisar huɗu a matsayin masu butulci. Misali da Kawu Sumaila da ya daɗe yana neman Sanata bai samu ba, har sai da ya haɗa tafiya tare da Kwankwaso.
Ana ganin Kwankwasiyya ka iya samun rauni, musamman a Kano ta Kudu, idan har aka tafi a haka. Kuma da ma tun a zaɓen 2023, Kwankwasiyya ba ta da ƙarfin a-zo-a-gani a yankin Kano ta Arewa.
Abun jira a gani shi ne ko Kwankwaso zai yafe wa ’yan majalisar, a tunkari zaɓen 2027 tare, tun da dai siyasa kasuwar buƙata ce.
Ko kuma zai zaɓi zama shi ƙadai gayya a zaɓe mai zuwa, kamar yadda ya sha gwadawa a baya tana kai masa.
Idan ko hakan ya zaɓa, tabbas za a doka siyasa, kuma a cikin biyu a yi ɗaya: Walau ya koya musu darasinta, ko kuma su nuna masa ƙarfinsu ya kawo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kawu Sumaila Kwankwasiyya Kwankwaso Siyasa yan majalisar Kawu Sumaila da Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
Sadeeƙ Umar da ake yi wa laƙabi da Mane, matashin ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne da yake tashen taka leda a rukunin ’yan dagaji a Jihar Kano.
Matashin, wanda tauraronsa ke haskawa a fagen tamola ya yi fice ne bayan da ya kafa wani sabon tarihi na zura ƙwallaye 10 a raga a wasanni 10 da ya buga tare da ba da taimako sau 6 wajen wasu ƙwallayen a rukuni gasar wasannin ’yan dagaji aji 1 da aka fi sani da Amateur 1 a Jihar Kano.
An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwaA cikin tattaunawarsa da Aminiya, Sadeeƙ Mane ya bayyana cewa, ƙwazo da sadaukar da kai ne suka taimaka masa wajen kafa wanna tarihi.
Sadeeƙ, wanda kamar sauran ‘yan wasa ya fara buga ƙwallon ne a cikin unguwa kafin daga bisani ya fara buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo da ke Unguwar Birget, Ƙaramar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano.
Daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo, Sadeeƙ ya koma taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Legend FC, inda a can ne bayan ya nuna bajinta a Gasar Cin Kofin Shugaban Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta SBS Waliyya da ke buga wasa a matakin Amauteur 1 ta ɗauke shi.
A kakar bana Saƙeeƙ ya kafa tarihi, inda ya buga wasanni goma kuma ya zura ƙwallaye goma a raga.
Wannan nasara da ya samu ta sa ya lashe kyautar ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa zura ƙallaye a raga a wannan shekara.
Haka kuma an zaɓi Saƙeed a matsayin ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa ƙwarewa a wannan matakin.
Da yake ƙarin bayani kan yadda ya samu nasarar zura ƙwallaye 10 a cikin wasanni 10, Sadeeƙ ya ce, “na buga wasanni 10 kuma na zura ƙwallaye 10 a ragar abokan karawa.
A cikin wasanni 10 ɗin na zura ƙwallayen ne a wasanni 8, wato wasa 2 kacal ne ban ci ƙwallo ba. Wannan ne ya sa na zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a gasar.”
Da yake amsa tambayar ko me ne sirrin wannan nasarori haka?
Sadeeƙ Umar sai ya ce: “Ka san an ce in ka ji wane ba banza ba, wato in ba a sha gumi ba a sha rana. Don haka na jajirce ne da ba wa kaina horo da kuma sanya juriya a zuciyata. Wato ina nufin bayan horon da ake yi mana a filin wasa, ni a karan kaina ina fita, in yi gudu da dadare da sauran wasanni na motsa jiki masu wahala don in saba wa kaina,” in ji Mane.
Ya ƙara da cewa, “wannan shi ya sa za ka ga in na shiga fili bana gajiya har a tashi. Haka kuma, wannan shi ne dalilin da ya sa ake yi min laƙabi da shahararren ɗan wasan ƙasar Senegal ɗin nan mai suna Sadio Mane, wato ganin irin salon wasanmu ɗaya ne, kai har ma wasu na cewa, wai mun yi kama ko a fuska.”
Sadeeƙ Mane ya bayyana wa Aminya cewa, burinsa shi ne wata rana ya zama kamar Sadio Mane wato ya fita ƙasashe Turai, ya buga wa manyan ƙungiyoyin ƙwallo ƙafa na duniya wasa.
“Kamar kowane matashin ɗan ƙwallo, ni ma babban burina shi ne in buga ƙwallo a ƙasashen Turai, in shahara kamar Sadio Mane. Ina ji a raina wata rana zan buga wa manyan ƙungiyoyi kamar Chealsea da Liɓerpool da Barcelona,” in ji matashi ɗan wasan.
Sai dai Sadeeƙ ya bayyana cewa, ba kamar sauran matasan ’yan ƙwallo ba da suke son shiga Turai gaba-gaɗi, shi yana da burin ya buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars kafin ya tafi ƙasashen Turai da ƙwallo.
“A gaskiya ni in so samu ne, na fi son in fara buga wa Kano Pillars wasa kafin in je Turai. Saboda tunda na taso, ina son Pillars sosai. Haka kuma ina ga a matsayina na ɗan Kano zai zamo abin alfahari a gare ni a ce wata rana na sanya wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillar riga, na ba da tawa gudunmawar,” in ji Mane.
Mane ya bayyana rashin samun haɗuwa da manajan masu ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa ƙasashen Turai, musamman a jihohin Arewa a matsayin wani babban ƙalubale da matasan ‘yan wasa masu hazaƙa ke gamuwa da shi a wannan yanki.
“Babban ƙalubalenmu a nan Kano da sauran jihohin Arewa shi ne wa zai taimake ka, ya haɗa kai da manajan da suke ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa Turai. Ka ga muna da matasa masu ƙwazo da basira sosai, sai dai ba ma samun wannan gatan. Ban san dalilin da ya sa manajojin ɗin ba sa son zuwa nan ba,” In ji Sadeeƙ Mane.