Aminiya:
2025-06-25@19:28:59 GMT

’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya

Published: 25th, June 2025 GMT

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai wa motar ’yan sanda hari a Zariya, inda suka harbe ɗaya daga cikinsu har lahira, tare da raunata wasu uku.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar Talata, a unguwar Dalan Waje da ke kan hanyar Galadimawa, a Ƙaramar Hukumar Zariya da ke Jihar Kaduna.

An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta

A cewar wani mazaunin yankin da ya shaida faruwar lamarin, motar ‘yan sandan na bin wata mota ƙirar Golf kafin a ji ƙarar harbe-harbe.

Nan take mutane suka fara kwanciya a ƙasa domin tsira da rayukansu.

Wannan hari ya girgiza mazauna yankin, inda suka ce ko da yake yankin ya daɗe yana fama da hare-haren ’yan bindiga, amma an daɗe ba samu hari ba.

A harin, an kashe wani ɗan sanda mai suna Nasiru Musa.

Ɗan sandan mazaunin ƙofar Kibo ne a cikin birnin Zariya.

Sauran da suka jikkata sun haɗa da direban motar ’yan sandan, Auwalu Hassan Ɗan Jos, wani ɗan-sa-kai mai suna Awwal Hassan, Iliyasu Ya’u da Salisu Mohammed.

An garzaya da su zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, Zariya, domin samun kulawar likitoci.

Da Aminiya ta tuntuɓi kakakin ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya ce yana wajen wani taron sanin makamar aiki, don haka bai da cikakken bayani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Ɗan Sanda hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia

Rundunar Sojin ƙasar Columbia ta tabbatar da cewa fararen hula sun yi garkuwa da dakarunta guda 57.

Janar Federico Alberto Mejía  na Rundunar ya sanar a ranar Lahadi cewa mutane kimanin 200 sun yi garkuwa da sojojin ne bisa umarnin ’yan tawayen FARC da suka addabi ƙasar.

Ta bayyana cewa al’ummar ƙasar suna fuskantar matsin lamba daga ’yan tawayen masu ɗauke da makamai.

Sanarwar ta ƙara da cewa an sace sojoji 31 a ranar Asabar, ragowar kuma ranar Lahadi.

Erik Rodríguez ya bayyana cewa sace sojojin na da alaƙa da kama wani jagoran ’yan tawayen kungiyar EMC da sojojin suka yi.

Ya ce a yayin da suke ƙoƙarin daukar sa a jirgi ne mutanen suka yi musu ƙawanya suka yi awon gaba su a yankin Kudu maso Yammacin Micay Canyon mai tsaunuka.

Ƙungiyar ’yan tawayen FARC ta addabi yankin Kudu maso Yammacin ƙasar, wanda ya yi ƙaurin suna wajen safarar miyagun ƙwayoyi a kusa da Lardin El Plateado.

Yankin ya yi fice wajen sarrafawa da safarar horar iblis, kuma yana cikin yana daga cikin wuraren da suka fi dama da tashin-tsahina a ƙasar ta Columbia.

A baya kungiyar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin kasar a shekarar 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha
  • Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia
  • Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
  • Matsayi ya yi maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe