Aminiya:
2025-10-13@18:08:22 GMT

’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya

Published: 25th, June 2025 GMT

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai wa motar ’yan sanda hari a Zariya, inda suka harbe ɗaya daga cikinsu har lahira, tare da raunata wasu uku.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar Talata, a unguwar Dalan Waje da ke kan hanyar Galadimawa, a Ƙaramar Hukumar Zariya da ke Jihar Kaduna.

An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta

A cewar wani mazaunin yankin da ya shaida faruwar lamarin, motar ‘yan sandan na bin wata mota ƙirar Golf kafin a ji ƙarar harbe-harbe.

Nan take mutane suka fara kwanciya a ƙasa domin tsira da rayukansu.

Wannan hari ya girgiza mazauna yankin, inda suka ce ko da yake yankin ya daɗe yana fama da hare-haren ’yan bindiga, amma an daɗe ba samu hari ba.

A harin, an kashe wani ɗan sanda mai suna Nasiru Musa.

Ɗan sandan mazaunin ƙofar Kibo ne a cikin birnin Zariya.

Sauran da suka jikkata sun haɗa da direban motar ’yan sandan, Auwalu Hassan Ɗan Jos, wani ɗan-sa-kai mai suna Awwal Hassan, Iliyasu Ya’u da Salisu Mohammed.

An garzaya da su zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, Zariya, domin samun kulawar likitoci.

Da Aminiya ta tuntuɓi kakakin ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya ce yana wajen wani taron sanin makamar aiki, don haka bai da cikakken bayani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Ɗan Sanda hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Ya ci gaba da bayanin cewa, “Da zan koma Kaduna sai ya ba ni takarda na kai wa Wazirin Katsina, Alhaji Isa Kaita. Na zo Kaduna na yi jarrabawa, bayan mun kare na koma gida ina sauraren sakamakon jarrabawar. Ba zan taba mantawa ba, ana zaune wajen Hawan Daba don tarbar Sarauniyar Ingila sai na sami telegiram mai cewa na ci jarrabawa ana nema na a Kaduna.

 

“Na fadawa mahaifina. Muka kintsa muka bar Katsina sai Kaduna, daga Kaduna muka tafi Legas. Da isa ta Legas sai na ga abokan nawa da suka sami nasarar wannan tafiyar duk ‘yan Kudu ne. Ni kadai ne dan Arewa kuma Bahaushe cikin daga cikin mu takwas

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique October 11, 2025 Daga Birnin Sin Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia October 11, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara