Aminiya:
2025-08-10@07:42:25 GMT

Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta

Published: 25th, June 2025 GMT

Kasar Iran ta zargi Isra’ila da kai mata hari a safiyar Talata bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da tsagaita wuta a tsakanin kasashen biyu.

“Gwamnatin Yahudawa ta ƙaddamar mana da hari har guda uku a ƙasar Iran har zuwa ƙarfe 9:00 na safiyar Talata,” kamar yadda gidan talabijin ɗin kasar Iran ya ambato Kakakin rundunar sojojin ƙasar yana faɗa.

Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Kafin sanar da tsagaita wutar dai duka bangarorin biyu sun kai wa juna munanan hare-hare cikin dare.

’Yan mintina kafin lokacin ya cika dai, makaman Iran masu linzami sun sauka a kan wani gida da ke birnin Beersheba na kudancin Isra’ila, inda ya kashe mutum huɗu.

Sojojin Isra’ila sun ce sun game makaman daga Iran aka harba su.

Rundunar tsaron Isra’ila (IDF) ta ce na’urorinta na aiki tarwatsa wasu makaman da aka harbo mata daga Iran, inda ta umarci mutane da su biya a cikin gidaje har zuwa abin da hali ya yi.

To sai dai Iran ta musanta kai harin.

Isra’ila dai ya sha alwashin mayar da martani kan abin da ta kira saba alkawarin yarjejeniyar da aka cimma.

A cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, Shugaban Trump ya ce kasashen biyu sun amince su dakatar da yaƙin cikin sa’o’i 24, inda ƙasar Iran za ta fara aiki da tsagaitawar.

Trump ya bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na diflomasiyya da zai kawo ƙarshen ci gaba da lalata yankin na Gabas ta Tsakiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila yaki

এছাড়াও পড়ুন:

Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin minista ba — Sarki Sanusi II

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya ce bai dace a riƙa bai wa mutanen da suka wawure dukiyar ƙasa manyan muƙaman gwamnati kamar ministoci ba.

A cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Sanusi II, ya bayyana damuwarsa game da yadda ’yan Najeriya ke son dukiya fiye da gaskiya da tarbiyya.

Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC

Ya ce al’umma na girmama masu kuɗi, ko da kuwa an san kuɗin haram ne.

“Ƙasar da ke bai wa mutanen da aka san sun wawure dukiyar ƙasa muƙamin minista, za ta ci gaba da tafiya a doro mara kyau,” in ji Sanusi.

“Ba ma jin kunya idan wani ɗan siyasa ya tara dukiya ta hanyar da ba ta dace ba, sai ma mu yi masa tafi.”

Sanusi ya ce mutane da dama yanzu na shiga siyasa ne don su tara kuɗi, ba don su yi wa jama’a aiki ba.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan shugabanni suna auna darajarsu ne da adadin gidajen da suke da su, jiragen sama masu zaman kansu, ko kuɗaɗe a asusun banki.

Ya ce ba su damu da irin kyakkyawan tasirin da suka yi wa al’umma ba.

Ya kuma ce rashin tarbiyya da gaskiya a tsakanin shugabanni na ƙara raunana tsarin gwamnati gaba ɗaya.

A cewarsa, wasu ba su damu da abin da mutane za su ce game da su ba muddin sun mallaki dukiya.

Yayin da yake tunawa da tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja, Murtala Muhammed, Sanusi ya ce Najeriya na buƙatar dawo da kyawawan ɗabi’u irin na shugabannin da suka gabace mu.

“Muna buƙatar daidaita ɗabi’unmu gaba ɗaya,” in ji shi.

“Ba wai shugaban ƙasa ko gwamnoni kaɗai ba ne za su canja ƙasa, kowa na da rawar da zai taka.”

Ya ƙara da cewa ’yan siyasa sun lalata tsarin aikin gwamnati, kuma Najeriya na buƙatar gina tsari mai ƙarfi da zai bai wa ma’aikatan gwamnati damar ƙin amincewa idan suka nemi su karya doka.

Sanusi, ya jaddada cewa kamata ya yi al’ummar Najeriya ta bai wa ɗabi’u kamar gaskiya, aiki tuƙuru, da tausayawa fifiko sama da tara dukiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • Iran da Masar sun jaddada wajabcin daukar matakan kawo karshen kisan kiyashi a Gaza
  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
  • Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
  • Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya  
  • An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II
  • Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin minista ba — Sarki Sanusi II