Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
Published: 25th, June 2025 GMT
Kasar Iran ta zargi Isra’ila da kai mata hari a safiyar Talata bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da tsagaita wuta a tsakanin kasashen biyu.
“Gwamnatin Yahudawa ta ƙaddamar mana da hari har guda uku a ƙasar Iran har zuwa ƙarfe 9:00 na safiyar Talata,” kamar yadda gidan talabijin ɗin kasar Iran ya ambato Kakakin rundunar sojojin ƙasar yana faɗa.
Kafin sanar da tsagaita wutar dai duka bangarorin biyu sun kai wa juna munanan hare-hare cikin dare.
’Yan mintina kafin lokacin ya cika dai, makaman Iran masu linzami sun sauka a kan wani gida da ke birnin Beersheba na kudancin Isra’ila, inda ya kashe mutum huɗu.
Sojojin Isra’ila sun ce sun game makaman daga Iran aka harba su.
Rundunar tsaron Isra’ila (IDF) ta ce na’urorinta na aiki tarwatsa wasu makaman da aka harbo mata daga Iran, inda ta umarci mutane da su biya a cikin gidaje har zuwa abin da hali ya yi.
To sai dai Iran ta musanta kai harin.
Isra’ila dai ya sha alwashin mayar da martani kan abin da ta kira saba alkawarin yarjejeniyar da aka cimma.
A cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, Shugaban Trump ya ce kasashen biyu sun amince su dakatar da yaƙin cikin sa’o’i 24, inda ƙasar Iran za ta fara aiki da tsagaitawar.
Trump ya bayyana yarjejeniyar a matsayin wani muhimmin mataki na diflomasiyya da zai kawo ƙarshen ci gaba da lalata yankin na Gabas ta Tsakiya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sojin kasar Sudan sun yi watsi da bukatar da kasar Amurka ta gabatar mata na dakatar da bude wuta, ta sha alwashin murkushe dakarun RSF wato kungiyar sojin sa kai ta kasar dake iko da mafiyawancin yankunan yammacin kasar Sudan
Wannan matakin yazo ne bayan taron gaggawa Da majalisar tsaron kasar ta gudanar wanda shugaban majalisar sojojin kasar janar Abdel fatah Al-burhan ya jagoranta inda suka sha alwashin murkushe dakarun kungiyar ta RSF.
Alburhan yayi alkawarin samun nasara yace wadanda suke yaki don kare hakkin alummarsu ba zaa yi nasara akan su ba,
Wadannan bayanan sun zo ne kwanaki kadan bayan da kungiyar ta RSF ta kwace garin al-fasher dake yammacin Darfur inda rahotanni suka bayyana irin kisan kare dangi da tayi da ya tilastawa fararen hula yin gudun hijira zuwa arewaci da kudancin Darfur.
Daga lokacin da yaki ya barke a watan Aprilun shekara ta 2023 tsakanin dakkarun kasar da dakarun kungiyar RSF an kashe dubban mutane kuma akalla mutane miliyan 13 ne suka tarwaste inda kungiyar RSF ke iko da jihohi 5 dake yankin Dafur
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani November 6, 2025 Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci