Aminiya:
2025-10-13@18:09:50 GMT

Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Published: 27th, June 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar.

Murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take.

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Ganduje, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya bayyana rashin lafiya a matsayin dalilin da ya da ya ajiye muƙaminsa.

Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.

Lokacin da ya kwashe a matsayin shugaban jam’iyyar na cike da cece-kuce da suka.

Dalilin murabus ɗinsa

Ko da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.

Haka kuma, an danganta murabus ɗinsa da zarge-zargen almundahana da karkatar da kuɗaɗe.

Wasu ’ya’yan jam’iyyar sun koka cewa ofishinsa na tilasta musu biyan kuɗi da yawa, musamman masu neman tikitin takara a Abuja.

Tasirin murabus ɗinsa ga jam’iyyar APC

Murabus ɗin Ganduje babban sauyi ne ga shugabancin jam’iyyar APC.

Yanzu haka, mutane da dama suna jiran su ji yadda jam’iyyar za ta shawo kan wannan lamari.

Har yanzu jam’iyyar APC ba ta fitar da wata sanarwa kan murabus ɗinsa ba.

Matsalolin da suka shafi Ganduje kan shugabancin jam’iyyar

A farkon shekarar 2024, wata kotu a Jihar Kano ta hana Ganduje ci gaba da kiran kansa da ɗan jam’iyyar APC, bayan wasu shugabannin jam’iyyar sun shigar da ƙara a kansa.

Daga baya kuma, wata kotu a Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu ke yi don a tsige shi daga shugabancin jam’iyyar.

Zamanin Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar cike yake da rikice-rikice, kuma murabus ɗinsa yanzu zai sanya dasa ayar tambayoyi domin neman wasu amsoshi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Murabus shugabancin jam iyyar murabus ɗinsa jam iyyar APC

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

 

Ta wadanne hanyoyi cutar Kansa ke farawa?

Kowace kwayar halitta ta jikin mutum akwai aikin da take yi, asalin kwayar halittar ta kan kasu kashi-kashi; suna mutuwa idan aka fitar da su ko kuma suka lalace, sai wata kwayar ta maye gurbinsu. A irin wannan lokaci ne, Kansar ke samun gurin zama sai ta zuba tata kwayar halittar ta kori asalin kwayar halittar da ke jikin Dan’adam, wanda hakan ke jawo matsaloli a sassan jikin da Kansar ta kama.

Saboda haka, kwayar cutar Kansa; ta kan watsu a sauran sassan jiki, misali Kansar huhu ta kan tafi cikin kasusuwa ta girma, a yayin da kwayar ta yadu; ana kiranta da suna ‘meh-TAS-tuh-sis’, ita kuma Kansar huhu idan ta tafi cikin kasusuwa; ana kiran ta da suna ‘Lung Cancer’ a turance. A bangaren likitoci, kwayar cutar Kansar da ta shiga cikin kashi; daidai ta ke da ta huhu, sai dai idan ta yadu a cikin kashin.

 

Banbance-banbancen cutar Kansa:

Wata Kansar ta kan yadu ne cikin gaggawa, yayin da kuma wata ta ke yaduwa a hankali a hankali, sannan kowacce ana iya yin maganinta ta hanyoyi daban-daban, wata ta hanyar tiyata kadai za a iya samun waraka; wata kuma ta hanyar shan magani.

Idan mutum yana dauke da Kansa, likita ya kan yi kokari wajen gano irin Kansar da yake dauke da ita. Mutanen da ke da cutar Kansa, ana yi musu magani ne gwargwadon irin yanayin wadda suke dauke da ita.

 

Wane matsayi cutar Kansa ta taka?

Duk wanda ke dauke da wannan cuta ta Kansa, likita zai so sanin matakin da ta kai, daga inda ta fara ana kiran sa a turance ‘Cancer Stage’, sannan matsayin da Kansar ta ke shi ne zai taimaka wajen sanin maganin da za a dora mai dauke da lalurar a kai.

Kowace irin Kansa, akwai gwajin da ake yi domin gano matasayin da ta kai. A dokar gwajin matakinta na farko da kuma mataki na biyu, na nuna Kansar ba ta yi karfi sosai ba. Mataki na uku da na hudu kuma yana nuna ta yadu sosai. Mataki na hudu shi ne makura wajen yaduwar ta.

 

Alamomin 20 Na Kamuwa Da Cutar Kansa:

1- Shashsheka da karancin numfashi

2- Tari da ciwon kirji, alama ce ta Kansar huhu ko ta bargo ciwon kirjin kan kasance daga kirjin zuwa kafada, sannan ya sauko zuwa hannu

3- Zazzabi da saurin kamuwa da ciwo, hakan na faruwa ne dalilin asalin kwayar halittar jinin mutum ta tabu

4- Fama wajen hadiye abu, wannan na nuni da an kamu da wannan cuta

5- Futowar kurji me ruwa a wuya, hammata da kuma gwiwa

6- Yawan zubda jini

7- Kasala da yawan gajiya

8- Kumburin ciki

9- Rashin sha’awar abu da kuma daukewar dandano

10- Ciwon ciki da mara

11- Fitar jini daga dubura

12- Rama lokaci guda

13- Yawan ciwon ciki

14- Nono ya yi ja ya kumbura alama ce ta ‘breast cancer’

15- Canjawar kan nono

16- Nauyi da kuma ciwo na fitar hankali a lokacin al’ada, wannan ita ma alama ce ta ‘uterus cancer’, ana bukatar yin hoto (transbiginal)

17- Kumburin fuska

18- Canjawar farce, zai iya kasancewa ‘lung cancer’, idan kuma ya kode ya yi fari to ‘liber cancer’ ne

19- Ciwon baya a bangaren dama, yana nuni da ‘liber cancer’ ko ‘breast cancer’

20-Fesowar kuraje a jikin mutum

Amma sai an je asibiti an ga likita kafin a tabbatar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Kiwon Lafiya Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace? October 5, 2025 Kiwon Lafiya Matsalar Tasgadewar Kashin Baya September 27, 2025 Kiwon Lafiya Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja September 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara