Aminiya:
2025-06-27@20:58:15 GMT

Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Published: 27th, June 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar.

Murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take.

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Ganduje, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya bayyana rashin lafiya a matsayin dalilin da ya da ya ajiye muƙaminsa.

Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.

Lokacin da ya kwashe a matsayin shugaban jam’iyyar na cike da cece-kuce da suka.

Dalilin murabus ɗinsa

Ko da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.

Haka kuma, an danganta murabus ɗinsa da zarge-zargen almundahana da karkatar da kuɗaɗe.

Wasu ’ya’yan jam’iyyar sun koka cewa ofishinsa na tilasta musu biyan kuɗi da yawa, musamman masu neman tikitin takara a Abuja.

Tasirin murabus ɗinsa ga jam’iyyar APC

Murabus ɗin Ganduje babban sauyi ne ga shugabancin jam’iyyar APC.

Yanzu haka, mutane da dama suna jiran su ji yadda jam’iyyar za ta shawo kan wannan lamari.

Har yanzu jam’iyyar APC ba ta fitar da wata sanarwa kan murabus ɗinsa ba.

Matsalolin da suka shafi Ganduje kan shugabancin jam’iyyar

A farkon shekarar 2024, wata kotu a Jihar Kano ta hana Ganduje ci gaba da kiran kansa da ɗan jam’iyyar APC, bayan wasu shugabannin jam’iyyar sun shigar da ƙara a kansa.

Daga baya kuma, wata kotu a Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu ke yi don a tsige shi daga shugabancin jam’iyyar.

Zamanin Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar cike yake da rikice-rikice, kuma murabus ɗinsa yanzu zai sanya dasa ayar tambayoyi domin neman wasu amsoshi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Murabus shugabancin jam iyyar murabus ɗinsa jam iyyar APC

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta mayar da na hannun damar Ministan Abuja Nyesom Wike, wato Samuel Anyanwu kan kujerarsa ta Sakataren jam’iyyar na ƙasa.

Mai riƙon muƙamin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Iliya Damagum ne ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Laraba.

Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara

Yayin taron dai, shugaban na tare da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Damagum ya ce yanke shawarar dawo da Anyanwu cikin kwamitin zartarwar jam’iyyar na ƙasa shawara ce mai wahalar gaske, amma ta sami goyon bayan mambobin kwamitin da dama.

Ya kuma sanar da cewa PDP ta soke taron kwamitinta na zartarwa da a baya aka yi yunkurin yi amma Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ba da shawarar dakatarwa.

Damagum ya kuma ce, “Za mu yi babban taron masu ruwa da tsaki a nan gaba, wanda daga nan ne za a tsara babban taron jam’iyyar.

“Anyanwu zai dawo kujerarsa ta Sakataren PDP na ƙasa, shi ya sa na ce shawara ce mai wahalar gaske. Kamar yadda INEC ta ce ba mu sanar da ita a kan lokaci ba, taron da za mu yi ranar 30 ga watan Yuni na masu ruwa da tsaki ne,” in ji shi.

A baya dai jam’iyyar ta dakatar da Anyanwu daga mukamin nasa sakamakon rikicin da ya dabaibaye ta wanda ta zargi Wiken da hannu a ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • Shugaban APC na ƙasa Ganduje ya yi murabus
  • Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
  • PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027