PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
Published: 25th, June 2025 GMT
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta mayar da na hannun damar Ministan Abuja Nyesom Wike, wato Samuel Anyanwu kan kujerarsa ta Sakataren jam’iyyar na ƙasa.
Mai riƙon muƙamin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Iliya Damagum ne ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Laraba.
Yayin taron dai, shugaban na tare da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.
Damagum ya ce yanke shawarar dawo da Anyanwu cikin kwamitin zartarwar jam’iyyar na ƙasa shawara ce mai wahalar gaske, amma ta sami goyon bayan mambobin kwamitin da dama.
Ya kuma sanar da cewa PDP ta soke taron kwamitinta na zartarwa da a baya aka yi yunkurin yi amma Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ba da shawarar dakatarwa.
Damagum ya kuma ce, “Za mu yi babban taron masu ruwa da tsaki a nan gaba, wanda daga nan ne za a tsara babban taron jam’iyyar.
“Anyanwu zai dawo kujerarsa ta Sakataren PDP na ƙasa, shi ya sa na ce shawara ce mai wahalar gaske. Kamar yadda INEC ta ce ba mu sanar da ita a kan lokaci ba, taron da za mu yi ranar 30 ga watan Yuni na masu ruwa da tsaki ne,” in ji shi.
A baya dai jam’iyyar ta dakatar da Anyanwu daga mukamin nasa sakamakon rikicin da ya dabaibaye ta wanda ta zargi Wiken da hannu a ciki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anyanwu
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Don haka, kwamishinan ya gode wa ƙungiyar bisa wannan ziyara tare da bayyana shirin Ma’aikatar na yin haɗin gwiwa da haɗin gwiwa ta fuskar horarwa, wayar da kan jama’a, da wayar da kan jama’a game da SGBƁ.
Tun da farko, Misis Achimugu ta bayyana cewa ziyarar bayar da shawarwarin ita ce kashi na biyu na ci gaba da wayar da kan jama’a, da bayar da shawarwari, koyan fasaha, da kuma shirin tallafa wa jama’a, wanda wani ɓangare ne na dabarun yaƙi da cin zarafin mata (SGBƁ) a Jihar Kogi.
Ta bayyana muhimmancin haɗa hannu da masu ruwa da tsaki, ma’aikatu, sassa, hukumomi (MDAs), ƙungiyoyi masu zaman kansu, da cibiyoyin gargajiya da na addini domin yaƙar matsalar SGBƁ, musamman a tsakanin marasa ilimi da tattalin arziki.
Maganar ta, “Kowa zai iya zama mai laifi kuma kowa zai iya zama wanda aka azabtar da SGBƁ ba tare da la’akari da ƙabila, addini da yanayin ƙasa ba. Muna kira da a canza tunani, a ƙara wayar da kan jama’a a yankunan karkara, matakan kariya da kuma buƙatar a tura masu laifin da ba su tuba ba zuwa gidan yari don nuna rashin haƙuri da gwamnati a kan SGBƁ.”
Daga baya ƙungiyar ta yi hulɗa da fadar Maigari ta Lokoja, Mai Martaba Sarki, Alhaji Ibrahim Gambo Kabir Maikarfi IƁ.
Maigari ya yi maraba da Tawagar PTCF zuwa Lokoja, garin da aka sani da zama ƙaramar Nijeriya saboda yawan ƙabilu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp