Aminiya:
2025-10-13@15:50:07 GMT

PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta

Published: 25th, June 2025 GMT

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta mayar da na hannun damar Ministan Abuja Nyesom Wike, wato Samuel Anyanwu kan kujerarsa ta Sakataren jam’iyyar na ƙasa.

Mai riƙon muƙamin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Iliya Damagum ne ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Laraba.

Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara

Yayin taron dai, shugaban na tare da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Damagum ya ce yanke shawarar dawo da Anyanwu cikin kwamitin zartarwar jam’iyyar na ƙasa shawara ce mai wahalar gaske, amma ta sami goyon bayan mambobin kwamitin da dama.

Ya kuma sanar da cewa PDP ta soke taron kwamitinta na zartarwa da a baya aka yi yunkurin yi amma Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ba da shawarar dakatarwa.

Damagum ya kuma ce, “Za mu yi babban taron masu ruwa da tsaki a nan gaba, wanda daga nan ne za a tsara babban taron jam’iyyar.

“Anyanwu zai dawo kujerarsa ta Sakataren PDP na ƙasa, shi ya sa na ce shawara ce mai wahalar gaske. Kamar yadda INEC ta ce ba mu sanar da ita a kan lokaci ba, taron da za mu yi ranar 30 ga watan Yuni na masu ruwa da tsaki ne,” in ji shi.

A baya dai jam’iyyar ta dakatar da Anyanwu daga mukamin nasa sakamakon rikicin da ya dabaibaye ta wanda ta zargi Wiken da hannu a ciki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Anyanwu

এছাড়াও পড়ুন:

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP October 11, 2025 Siyasa Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu October 9, 2025 Labarai Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas October 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP