Aminiya:
2025-06-27@16:54:27 GMT

Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike

Published: 27th, June 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya tabbatar da cewa tattaunawar da suka yi da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ta kawo ƙarshen duk wata rigima da ke tsakaninsa da Gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara.

A daren ranar Alhamis ne Shugaba Tinubu, ya jagoranci wani zaman sulhu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, tsakanin Wike da Gwamna Fubara da kuma wasu daga cikin ’yan majalisar Ribas da aka dakatar.

NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe  Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji

Bayan ganawar, Wike ya yi magana da manema labarai, inda ya tabbatar da kawo ƙarshen rikicinsa da Fubara.

“Dukkaninmu mun amince mu yi aiki tare da Gwamna, kuma shi ma ya amince zai yi aiki da mu. Dukkanninmu ’yan gida ɗaya ne.

“Rigimarmu ta daɗe, amma zamanmu na ranar Alhamis ya kawo ƙarshenta. Dama ɗan Adam yana iya samun saɓani, amma daga baya a sasanta.”

Ya ƙara da cewa: “Kuma yau ne muka kammala komai, mun zo mun shaida wa Shugaban Ƙasa cewa mun daidaita. Don haka a gare ni, komai ya wuce.”

Wike, ya kuma yi kira ga mabiyansa da su kwantar da hankali tare da haɗa kai don ciyar da Ribas gaba.

“Ina kira ga kowa da kowa da mu haɗa kai da sauran jama’a. Babu sauran rigima, babu wani abu da za a sake yin faɗa a kai.”

Abin da rikicin ya haifar

A baya dai rikicin siyasa a Jihar Ribas, ya haifar da barazanar tsige Gwamna Fubara a watan Oktoban 2024, yayin daga bisani Shugaba Tinubu ya ayyana  dokar ta-ɓaci a watan Maris a jihar

Sai dai yanzu ɓangarorin sun ce komai ya wuce, kuma za su ci gaba da aiki tare domin ci gaban jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fubara Saɓani Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum

Ɗaya daga cikin baƙin da suka tafi ɗaurin aure daga Zariya, Abbas Rufa’i, ya bayyana yadda ya kuɓuta daga harin da wasu matasa suka kai musu a Ƙaramar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato.

A cewarsa, “Da muka tsaya a hanya domin yin tambaya, na fito daga motar domin neman hanya. Amma sai na ga yadda mutanen da ke wajen suka fara mana wani irin kallo.

Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma 1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

“Na ji ɗaya daga cikinsu yana cewa, ‘a kashe su gaba ɗaya, a ƙone motar.’”

Rufa’i ya ƙara da cewa, “Na cire rigata, na shiga cikin daji har na sai da na samu wani mai babur, na ce masa ya kai ni wajen ‘yan sanda. Amma da muka isa wajen wasu sojoji, sai na ce ya tsaya, na sanar da su abin da ya faru.”

Ya bayyana cewa sojojin sin bi shi zuwa wajen, inda suka ceto mutane 18 da suka jikkata, yayin da wasu sun rasu.

Za mu biya diyya – Gwamnatin Filato

Kwamishinar Yaɗa Labarai ta Jihar Filato, Joyce Ramnap, ta ce gwamnati za ta biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.

Ta ce, “Za mu biya diyya. Amma muna jiran rahoton ‘yan sanda kafin mu ɗauki mataki.”

’Yan majalisa sun buƙaci a kama waɗanda suka aikata laifin

Majalisar Wakilai ta buƙaci Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, Shugaban DSS da Hafsan Sojin Ƙasa su kama waɗanda suka aikata kisan.

Hon. Sadiq Ango Abdullahi ya ce, “Rashin kama masu laifi yana ƙara kawo rashin gaskiya da ƙarancin amana ga gwamnati.”

Kowa yana da ’yancin yin tafiya — Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce, “Doka ta bai wa kowa ’yancin zirga-zirga a Najeriya. Gwamnoni su tabbatar da hakan.”

Ya godewa al’ummar Kudan da suka zauna lafiya duk da irin halin da suka tsinci kansu a ciki.

Za a hukunta waɗanda suka aikata laifin – Gwamnatin Filato

Joyce Ramnap ta ce an kama mutum 22 da ake zargi da hannu a harin. “Za mu hukunta duk wanda aka samu da laifi,” in ji ta.

Wannan laifi abu ne da aka tsara — Ƙungiyar Musulmai

Ƙungiyar Musulmai ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta ce, “Ba kuskure aka yi ba. Wannan kisan an shirya shi ne. Idan ba a hukunta masu laifin ba, hakan na iya jawo ramuwar gayya.”

Waɗanda suka aikata wannan laifi dabbobi ne — Ƙungiyar CAN

Ƙungiyar Kiristoci ta Arewa ta ce, “Kisan da aka yi wa waɗanda ba su da laifi ba shi ne mafi muni cikin ɗabi’ar ɗan Adam. Wannan rashin imani ne kuma bai dace ba.”

Wannan kisan laifi ne da aka shirya — Ƙungiyar Dattawan Arewa

NEF ta ce, “Wannan ba kuskure ba ne, laifi ne da aka tsara. Yana nuna irin matsalolin da ke damun Arewa.”

Ƙungiyar ta buƙaci a hukunta duk masu hannu cikin lamarin.

Kisan ’yan ɗaurin auren da suka taso daga garin Zariya zuwa Filato, ya tayar da ƙura a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke Allah-wadai da kisan.

Yanzu haka dai an zuba wa jami’an tsaro da gwamnati ido don ganin irin matakin da za a ɗauka kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Bejjo Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara