Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
Published: 26th, June 2025 GMT
Firaministan kasar Sin Li Qiang ya ce, kasarsa a shirye take ta rarraba fasahohinta na ainihi, da dabarunta na kirkire-kirkire tare da sauran sassan kasa da kasa. Li Qiang ya bayyana hakan ne cikin jawabinsa na bude taron shekara-shekara, na sabbin jagorori karo na 16, wato dandalin tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos a takaice, wanda aka bude yau Laraba a birnin Tianjin na kasar Sin.
Li ya kara da cewa, Sin na da karfin gwiwa, da ikon wanzar da ci gaban tattalin arzikinta, tana kuma kara kaimin zama kasa mai babban matsayin samun kudin shiga, yayin da ake kara daga matsayin sayayya bisa kyakkyawan yanayi a kasar, wadda ita ce ta biyu a girman kasuwar sayayya a duniya.
Firaministan na Sin ya kuma yi kira ga kasashen duniya, da su aiwatar da managartan matakan bunkasa hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki da cinikayya. Ya ce hakan na nufin rungumar matakai na hakika, don kare tsarin cinikayya cikin ’yanci, da cudanyar mabanbantan sassa, da goya baya ga daidaitaccen tsarin raya tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Tsaron Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza
Kwamitin Tsaro Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Amurka ta bukaci duba kudurin da aka gabatar na neman kafa rundunar kasa da kasa a Gaza
Rahotannin daga Amurka sun bayyana cewa: Gwamnatin Amurka ta Trump tana neman amfani da rikicin Gaza wajen kwace makaman kungiyar Hamas da take amfani da ramuka wajen yakar ‘yan sahayoniyya, don aiwatar da wani tsari na kwace makamai daga hannun ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa.
A ƙarƙashin tutar tsaro da kwanciyar hankali, Amurka, da kuma Isra’ila, suna ƙoƙarin kafa sabon tsari a Gaza wadda ke neman murkushe ‘yan gwagwarmaya, tare da tabbatar da tsarin babakeren ‘yan mamaya karkashin wani tsari mai sauƙi, da zai buɗe sabon babi na iko a kan yankin.
A tsakiyar tambayoyi game da manufofin Amurka da Isra’ila game da makomar yankin Gaza, Amurka na gabatar da daftarin kuduri ga Kwamitin Tsaro don tallafawa shirin shugaban Amurka Donald Trump, wanda ake tallata shi a matsayin shirin zaman lafiya ga yankin Gaza.
An rarraba daftarin, wanda ke kira da a kafa rundunar ƙasa da ƙasa ta wucin gadi a yankin, ga membobin Kwamitin Tsaron, da kuma Saudiyya, Masar, Qatar, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Turkiyya, a hukumance, domin samun goyon bayan yankin, a cewar tawagar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya. Amurka ta yi da’awar cewa; Manufar ita ce don kawo karshen yakin da kuma sake gina Gaza, amma daftarin kudurin ya ba ta cikakken iko ta gudanar da yankin ta hanyar rundunar zartarwa wadda ba ta da cikakken iko a karkashin ikon Majalisar Dinkin Duniya kuma tana aiki tare da Masar da Isra’ila. Haka kuma tana goyon bayan abin da ake kira Majalisar Zaman Lafiya, wacce Trump ke jagoranta, don gudanar da harkokin mulki na wucin gadi da sake gina Gaza har zuwa karshen shekara ta 2027.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci