Aminiya:
2025-06-26@12:05:20 GMT

NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su

Published: 26th, June 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.

 

Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su.
Sai dai a wannan zamani ‘yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikin su ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita.


Ko wadanne matakai ya kamata ‘yan Najeriya su ringa dauka wajen kare kan su da ma lafiyar jikin su?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A YAU na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda ‘yan Najeriya zasu dinga kula da lafiyar jikin su.

Domin sauke shirn, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kula da lafiya lafiyar jiki

এছাড়াও পড়ুন:

Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce sama da mutane 40 ciki har da ma’aikatan kiwon lafiya aka kashe a harin da aka kai wani asibiti da ke Sudan a ƙarshen mako.

Ofishin hukumar ta WHO da ke Sudan, ya ce daga cikin waɗanda suka mutu akwai ƙananan yara shida da jami’an kiwon lafiya biyar, sannan kuma an yi wa ginin asibitin mummunar ɓarna.

EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn Yarjejeniyar tsagaita wutar Isra’ila da Iran ta samu tasgaro

RFI ya ruwaito cewa an dai kai harin ne kan Asibitin Al Mujlad da ke a yammacin Kordofan a ranar asabar da ta gabata, kusa da inda ake fafatawa tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF, a yaƙin da suke yi tun a watan Afrilun shekarar 2023.

Shugaban WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya nemi a dakatar da kai wa cibiyoyin kiwon lafiya hari, duk da cewa bai ambaci sunan ɓangaren da ake zargi da kai wannan hari ba.

Sai dai ƙungiyoyin kare hakkin ɗan adam sun zargi wani jigin yaƙin sojojin Sudan marar matuƙi da kai wannan hari, da wata sanarwa da aka fitar a ƙarshen mako ta ce mutunen da suka mutu sun kai 9.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha
  • Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO
  • EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn
  • An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
  • NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu