Leadership News Hausa:
2025-06-26@23:35:58 GMT

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Published: 26th, June 2025 GMT

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Shettima zai kuma ziyarci manyan masana’antu da gonaki a sassa daban-daban na Habasha.

Masana’antun sun haɗa da Adama Industrial Zone, Mojo Poultry Farm, Shera Dibandiba Mojo Family Farm, Lume Avocado Nursery, da Bishoftu Pea Youth Farm.

Wannan ziyara na da nufin ƙarfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da Habasha, musamman a fannin noma da masana’antu.

Firaminista Abiy zai kuma shirya wata liyafa ta musamman a Fadar Shugaban Kasar domin girmama Shettima da tawagarsa, a matsayin alamar ƙarfafa dangantakar diflomasiyya da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu.

Nijeriya da Habasha na da daɗaɗɗen tarihin aiki tare, musamman a fannonin tsaro, kiyaye zaman lafiya da kuma haɗin gwiwar tattalin arziƙi.

Wannan ziyara na da burin ƙarfafa wannan dangantaka da kuma samar da damar haɗin gwiwa a fannin sauyin yanayi, wadatar abinci, da ci gaban masana’antu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Yanzu sun sake nuna sha’awarsu, suna fatan ɗaukar ɗan wasan mai shekaru 28.

Manchester United ma ta nuna sha’awar ɗaukar Ndidi idan har ta sayar da Casemiro, wanda ake raɗe-raɗin zai koma Saudiyya.

A watan Janairu, Monaco da ke gasar Ligue 1 ta yi ƙoƙarin ɗaukar Ndidi, amma Leicester ta ƙi amincewa.

Hakazalika, akwai ƙungiyoyi daga Saudiyya da ke son ɗaukarsa kuma suna shirin ba shi albashi mai tsoka, amma Ndidi yafi son ci gaba da buga wasa a Turai.

Ndidi ya koma Leicester City a watan Janairun 2017 daga kulob ɗin Genk na Belgium.

Ya lashe kofin FA Cup da Leicester a 2020, kuma ya zura ƙwallaye 11 a cikin wasanni 252 da ya buga wa ƙungiyar cikin shekaru takwas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS
  • Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu