Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Published: 27th, June 2025 GMT
Taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos, wanda aka gudana a tsakanin ranar 24 zuwa ranar 26 ga watan nan da muka ciki, a birnin Tianjin na kasar Sin, ya samu halartar wakilai kimanin 1800 daga kasashe da yankuna sama da 90, adadin da ya kai koli cikin tarihi. Kamar yadda babban daraktan dandalin Davos Borge Brende ya bayyana, “in muka duba yanayin kasashen duniya, za a gane cewa, wakilai a fannonin masana’antu da kasuwanci na kasashe da dama, suna fatan zuba jari a kasar Sin, tare da zurfafa hadin gwiwar cinikayya dake tsakaninsu da kasar Sin.
A halin yanzu, kasuwannnin kasar Sin suna ci gaba da samun kyautatuwa da karuwa, lamarin da ya samar da damammaki ga bunkasar hadin gwiwar cinikayya a tsakanin kasa da kasa. Ci gaba da yin kirkire-kirkire a kasar Sin, ya samar da sabon karfi na neman samun bunkasa. A ciki kuma, bunkasar fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI ta janyo hankulan jama’a cikin taron Davos. Masana na ganin cewa, idan muka yi amfani da fasahohin da abin ya shafa kan aikin nazarin sabbin kayayyaki, zai ninka saurin gudana da ayyukanmu sau 100 har ma zuwa sau 1000. Kuma kasar Sin za ta taka muhimmiyar rawa cikin wannan babban sauyi.
Haka kuma, cikin farkon watanni 5 na bana, an kafa sabbin kamfanoni masu jarin waje guda 24,018 a cikin kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 10.4 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara. Kamfanonin kasashen duniya sun nuna fatansu na hada kai da kasar Sin. Kamar yadda tsohon firaministan kasar Burtaniya Tony Blair ya bayyana a yayin taron Davos cewa, “ya kamata a ci gaba da tuntubar kasar Sin a kai a kai.” (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Mali: An Dakatar Da Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
Hukumar da take kula da harkokin watsa labaru a kasar Mali ta sanar da dakatar da ayyukan wasu kafafen watsa labarun kasar Faransa biyu a cikin kasar.
Wadannan kafafen watsa labarun dai su ne LCI da TF1 saboda zarginu da watsa gubatattun labaru akan matsalar makamashi da ake fama da ita.
TF1 dai tashar talabijin din Faransa ce mai zaman kanta da take watsa shirye-shiryenta a kasashe mabanbanta.
Ita kuwa LCI ( La Chaine Info) tashar labarai ce wacce take a karkashin TF1.
Hukumar dake kula da sanarwa a cikin kasar ta Mali ( HAC) ta rubuta wata wasika zuwa ga kafafen watsa labaru a ranar 13 ga watan Nuwamba wacce kuma a wannan makon mai karewa ne aka fito da ita fili, da a ciki ta bayyana dakatar da ayyukan kafafen watsa labarun guda biyu na TF1 da LCI,bisa zargin cewa a ranar 9 ga watan Nuwamba sun watsa labarun da ba a tantance gaskiyarsaba, wanda kuma na kazon kurege ne.
Wasikar ta hukumar kasar ta Mai ta ambaci misalai uku da kafafen watsa labarun su ka watsa da su ka kunshi cewa: “ Mahukuntan soja a Mali sun hana sayar da man fetur.” “An killace biranen Kayes da Nioro baki daya.” “ Yan ta’adda sun gab da kwace iko da birnin Bamako.:
Wadannan kafafen watsa labarun uku dai ba su yi wani Karin bayani akan wannan zargin da ake yi musu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Isa Chiroma Mafaka Ta Wucin Gagi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci