Aminiya:
2025-09-24@11:14:17 GMT

Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump

Published: 25th, June 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce wakilan ƙasarsa za su gana da na Iran domin ci gaba da tattaunawa kan makaman nukiliyarta a mako mai zuwa.

“Za mu tattauna da Iran a mako mai zuwa, ƙila mu ƙulla yarjejeniya ko kuma akasin haka, ba na ce ba,” in ji shi yayin jawabinsa a taron ƙasashe na ƙungiyar ƙawancen tsaro ta NATO da ake yi a ƙasar Netherlands.

’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano

“Ba su daɗe da gama yaƙi ba, yanzu za su ci gaba da harkokinsu. Ban damu dole sai na ƙulla wata yarjejeniya da su ba,” a cewarsa.

A jiya Talata ce Trump ya soki Isra’ila da Iran, bayan zargin ƙasashen biyu da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla.

Lamarin na zuwa ne bayan ɓullar rahoton kai wa juna hari daga dukkan ƙasashen biyu, duk da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ’yan sa’o’in da suka gabata.

Trump ya ce ƙasashen sun daɗe suna faɗa da juna, kuma a wannan mataki ana iya cewa ba su ma san abin da suke yi ba.

Ya ce: “Ba abin da muke so ke nan ba, ina tabbatar muku cewa ina fushi da abin da suka aikata.”

Shugaba Trump ne mutum na farko da ya fara sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ilan da Iran, bayan shafe kwana 12 suna kai wa juna hare-hare.

Sai dai Iran ta musanta sanarwar da Trump ya yi cewa ta amince da tsagaita wuta a yaƙinta da Isra’ila, inda ta ce ƙofarta a buɗe take don dakatar da yaƙin, matuƙar Isra’ila ta dakatar da kai mata hari.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ne ya yi wannan jawabi, a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X a wannan Talata, yana mai cewa ya zuwa yanzu babu wata matsaya da suka cimma ta tsayar da wannan yaki, har sai Isra’ila ta fara dakatar da farmakinta a Iran, da ƙarfe 4 agogon Tehran, sannan Iran za ta mayar da wukarta cikin kube.

Tun cikin dare Litinin wayewar gari Talata ne Trump ya yi shelar cewa Isra’ila da Iran sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta na mataki-mataki daga ƙarfe 4:00 agogon GMT ranar Talata, da zummar kawo ƙarshen mummunan tashin hankali da aka shafe kusan makonnin biyu ana yi.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce yarjejeniyar ta nemi “cikakkiyar tsagaita wuta,” inda Iran za ta fara daina aiki [kai hare-hare], sannan Isra’ila za ta daina bayan sa’o’i 12.

Ana sa ran tsagaita wutar zai kasance “ƙarshe a hukumance” ga abin da Trump ya kira “Yaƙin kwanaki 12.”

“Bisa zaton cewa komai zai tafi yadda ya kamata, zan so na taya ƙasashen biyu murna, Isra’ila da Iran, game da kasancewa da ƙarfin hali da bajinta da kuma basirar kawo ƙarshen abin da ya kamata a kira “Yaƙin kwanaki 12,” kamar yadda Trump ya wallafa.

Rikicin ya ɓarke ranar 13 ga watan Yuni ne a lokacin da Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare kan wuraren soji da nukiliya da kuma fararen-hula a Iran ciki har da tashar inganta yuraniyom ta ƙarƙashin ƙasa da ke Fordo.

Tehran ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami kan wurare a Isra’ila, lamarin da ya janyo jerin ramuwar gayya da ya ta ƙasashen biyu suka fara kai hare-hare kan juna kai-tsaye.

Tashin hankali ya ƙaru a lokacin da Amurka ta yi tarayya da Isra’ila wajen kai hare-hare ranar 22 ga watan Yuni, inda ta kai hare-hare kan tashoshin nukiliyar Iran uku lamarin da ya sa makami mai linzamin Iran ya kai hari kan sansanin sojin saman Amurka na Al Udeid da ke ƙasar Qatar.

Trump ya haƙiƙance cewa hare-haren da suka kai sun tarwatsa tashoshin nukiliyar na Iran, tare da cewa jami’an ƙasar ba su iya kwashe wani abu daga tashoshin ba “saboda abubuwa ne masu wuyar kwashewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila nukiliya yarjejeniyar tsagaita wuta kai hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

Ya zuwa ranar 23 ga watan Satumba agogon Beijing, kasashe 152 cikin 193 na Majalisar Dinkin Duniya sun amince da Falasdinu a matsayin kasa. A cikin kasashe biyar masu kujerun dindindin a kwamitin sulhun MDD, Amurka ce kadai ba ta amince da kafuwar kasar Falasdinu ba. Wannan guguwar ta amincewa da kafuwar kasar Falasdinu ta sanya Amurka da Isra’ila sun zama saniyar ware a fannin diflomasiyya game da batun rikicin Falasdinu da Isra’ila.

Wata kuri’ar jin ra’ayoyin jama’a da CGTN ta gudanar a duniya ta nuna cewa kashi 78.2 cikin 100 na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu sun yi imanin cewa, babbar hanyar warware matsalar Falasdinu ita ce aiwatar da shawarar “kafa kasashe biyu”, wadda kuma ita ce ginshikin samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya. Kashi 81.8 cikin 100 kuma sun bayyana cewa, “kafa kasa mai cin gashin kanta, mai cikakken ‘yanci ta Falasdinu bisa kan iyakokin da aka shata a shekarar 1967, tare da gabashin Kudus a matsayin babban birninta” ta zama wata matsaya da aka cimma a tsakanin kasashen duniya.

A cewar bayanai daga hukumomin kiwon lafiya na Gaza, hare-haren sojojin Isra’ila a Gaza sun yi sanadin mutuwar mutane 65,283 tare da jikkata wasu 166,575 tun bayan sabon rikicin da ya barke tsakanin Isra’ila da Falasdinu a ranar 7 ga watan Oktobar shekarar 2023. A kuri’ar jin ra’ayoyin, kashi 90.8 cikin 100 na wadanda suka yi Allah-wadai da ta’asar da Isra’ila ke tafkawa, kuma sun yi imanin cewa, ya kamata Isra’ila ta gaggauta dakatar da hare-harenta na soji a zirin Gaza. Kazalika, kashi 92.1 cikin 100 sun yi kira ga kasashen duniya da su dauki mataki tare da yin taron dangi wajen taka birki ga farmakin sojojin Isra’ila a Gaza. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi; Tattaunawa Tsakanin Iran Da Norway Kan Kyakkyawar Alakar Da Ke Tsakaninsu
  • Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran
  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno
  • Hindi: Amurka Da Kasashen Yamma Ba Sa Son A Dakatar Da Bude Wuta A Gaza.
  • Iran Da Rasha Zasu Rattaba Hannun Kan Batun Gina Wasu Tashoshin Nukiliya.
  • Hamas ta bukaci kasashen duniya da MDD su mayar da Isra’ila saniyar ware
  • Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram