’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
Published: 25th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, sun kashe ’yan fashi biyu, sannan sun kama wasu biyu a unguwar Makera da ke Kakuri.
Wannan ya biyo bayan musayar wuta da jami’an tsaro suka da ’yan fashin.
Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarentaRundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:10 na dare, bayan da suka samu kiran gaggawa daga mazauna unguwar Gashash a Barnawa.
Rahotanni sun ce ’yan fashi guda takwas sun shiga wani gida ɗauke da bindigu da makamai, sun sace wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki.
Bayan kiran gaggawar, DPO na Barnawa, Kakuri da Sabon Tasha tare da sojoji daga Rundunar 312 Artillery Regiment suka bi ’yan fashin har titin Makera.
Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya ce, “Da ’yan fashin suka ga jami’an tsaro, sai suka fara harbi.
“Wannan ya jawo musayar wuta, inda aka kashe biyu daga cikinsu sannan aka kama biyu da ransu.”
Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar gida, harsasai da wasu makamai.
Sannan sun dawo da kayan da aka sace ciki har da wayoyi bakwai, agoguna uku, kwamfutoci biyu da sauransu.
A lokacin musayar wutar, ɗan sanda ɗaya ya samu rauni amma an miƙa shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya jinjina wa jami’ansa kan yadda suka yi aiki cikin gaggawa tare da haɗin kai da sojoji da DSS.
Ya ce rundunar ta ƙudiri aniyar kare jihar daga miyagu.
Ya kuma roƙi al’umma da su riƙa sanya idanu tare da kai rahoton duk wani abun zargi.
Rundunar ta ce tana ci gaba da neman sauran ‘yan fashin da suka tsere.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi musayar wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
Daya daga cikin manyan ’yan bindigar da suka addabi Najeriya, Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a wani harin kwanton bauna da ya kai a jihar Zamfara ranar Lahadi.
Bayanai sun nuna daga cikin wadanda aka kashe din har da wasu jami’an hukumar tsaro ta DSS su hudu da kuma wani tubabben dan bindiga da yanzu yake aikin bayar da bayanai ga jami’an tsaro, Bashar Maniya.
Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa an kai harin ne a kusa da Rugar Chida, wani kauyen da mahaifin Bello Turjin ke rike da sarautar gargajiya.
Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027 An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a NijeriyaAn dai yi wa jami’an da ke tafiya a cikin motoci biyu da babura kwanton baunar ne a yankin wanda ya shafe mako biyu babu sabis din waya saboda aikin da sojoji suke a ciki.
Wata majiya a yankin ta tabbatar wa Aminiya cewa harin ya daga musu hankali matuka kuma an shirya shi yadda ya kamata.
Majiyar ta ce, “An mamaye su. Bello Turji da yaransa sun kashe mutum 40 daga cikinsu sannan suka kwace ababen hawan da suke kai.
“Turji ya ji dadin harin sosai musamman saboda Bashar Maniya na cikin wadanda aka kashe, wanda tun a baya dama babban abokin hamayyarsa ne kafin ya tuba daga ta’addancin,” in ji majiyar.
A cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an ga Bello Turji yana murna tare da nuna gawarwakin mutanen, ciki har da ta Bashar Maniya, yana rera wakokin cin nasara.
“Wannan ce gawar Kwamandan da ya jagoranci harin,” kamar yadda aka jiyo Turjin yana bayyanawa a cikin bidiyon.
Daga bisani dai an kwaso gawarwakin mutanen tare da gudunmawar sojojin sama, yayin da wadanda suka jikkata kuma aka garzaya da su asibiti.
Wani jami’in tsaro da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi da abin takaici da za a iya kauce masa matukar ana aiki tare tsakanin jami’an tsaro da mutanen gari.
Bayanai dai sun nuna gabanin kisan mayakan, an kashe ’yan bindiga yaran Bello Turji sama da 30 a wata ba-ta-kashi da aka yi tsakanin yaran Turjin da na Maniya.