’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
Published: 25th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, sun kashe ’yan fashi biyu, sannan sun kama wasu biyu a unguwar Makera da ke Kakuri.
Wannan ya biyo bayan musayar wuta da jami’an tsaro suka da ’yan fashin.
Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarentaRundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:10 na dare, bayan da suka samu kiran gaggawa daga mazauna unguwar Gashash a Barnawa.
Rahotanni sun ce ’yan fashi guda takwas sun shiga wani gida ɗauke da bindigu da makamai, sun sace wayoyi, kwamfutoci da sauran kayayyaki.
Bayan kiran gaggawar, DPO na Barnawa, Kakuri da Sabon Tasha tare da sojoji daga Rundunar 312 Artillery Regiment suka bi ’yan fashin har titin Makera.
Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya ce, “Da ’yan fashin suka ga jami’an tsaro, sai suka fara harbi.
“Wannan ya jawo musayar wuta, inda aka kashe biyu daga cikinsu sannan aka kama biyu da ransu.”
Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga ƙirar gida, harsasai da wasu makamai.
Sannan sun dawo da kayan da aka sace ciki har da wayoyi bakwai, agoguna uku, kwamfutoci biyu da sauransu.
A lokacin musayar wutar, ɗan sanda ɗaya ya samu rauni amma an miƙa shi asibiti inda yake samun kulawar likitoci.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya jinjina wa jami’ansa kan yadda suka yi aiki cikin gaggawa tare da haɗin kai da sojoji da DSS.
Ya ce rundunar ta ƙudiri aniyar kare jihar daga miyagu.
Ya kuma roƙi al’umma da su riƙa sanya idanu tare da kai rahoton duk wani abun zargi.
Rundunar ta ce tana ci gaba da neman sauran ‘yan fashin da suka tsere.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi musayar wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
A ranar Juma’a da yamma, wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun tare motar haya a mararrabar Ogbabo, kan titin Itobe-Anyigba a jihar Kogi, inda suka yi awon gaba da fasinjoji 9. Direban motar da wasu fasinjoji 6 kuwa sun tsere ba tare da an sace su ba.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:20 na yamma a yankin ƙaramar hukumar Ofu, lokacin da ƴan bindigar suka fito daga daji suka tare titin. Sun tilasta direban motar Toyota mai ɗauke da fasinjoji tsayawa, sannan suka yi harbi cikin iska domin tsoratar da mutane. Direban motar, Sunday Okechi, ya yi dabara ya tsere tare da wasu fasinjoji 6, yayin da sauran 9 suka faɗa hannun ƴan bindigar da suka tafi da su cikin daji.
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A KoginNisan wurin da aka sace fasinjojin ya yi kusan mita 300 kacal daga shingen Sojoji na irin Ogbabo-Ochadamu. Jami’an tsaro sun isa wurin cikin gaggawa, inda suka tarar da motar haya mai lambar ENZ-55 XS da wata Toyota Carina ‘E’ a ajiye. An fara aikin ceto tare da haɗin gwuiwar ƴansanda, da Sojoji, da ƴan sa-kai da mafarauta domin gano masu laifin da kuma kuɓutar da waɗanda aka sace.
Kakakin rundunar ƴansanda jihar, SP Williams Ovye Aya, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran jami’an tsaro don ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka aikata laifin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp