Aminiya:
2025-06-27@00:47:36 GMT

Ronaldo ya tsawaita kwantaraginsa a Al Nassr

Published: 27th, June 2025 GMT

Cristiano Ronaldo ya sanya hannu kan yarjejeniyar tsawaita kwatiraginsa da shekara biyu a ƙungiyar Al Nassr  da ke buga gasar Saudi Pro League.

Wannan dai na nufin kyaftin din na tawagar Portugal zai ci gaba da zama a ƙungiyar har 2027, lokacin da zai kai shekara 42 a duniya.

Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya

Al-Nassr ta bai wa Ronaldo kwantiragi mafi tsada a tarihin wasanni, inda ya rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fam miliyan 24.

5 ($33.7m), lamarin da zai ba shi damar samun albashin da zai rika karbar sama da fam miliyan a duk kwana biyu.

Ɗan wasan mai shekara 40 ya je Al Nassr ne a Disamban 2022, bayan raba gari da Manchester United.

A ƙarshen watan Yunin da muke ciki ne kwantiraginsa na farko zai ƙare a ƙungiyar da ke Saudiyya.

Bayan sanya hannun ɗan wasan wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar ya ce “An buɗe sabon babin buri da sha’awar ci gaba da kafa tarihi tare” a shafinsa na Instagram.

Duk da cika shekaru 40, Ronaldo ya ci gaba da taka rawar gani, inda a kakar wasan da ta gabata ya zura kwallaye 35 a wasanni 41 da ya buga a duk gasa, lamarin da ya ba shi damar karewa a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar Saudi Pro League a shekaru biyu ke nan a jere.

Ronaldo wanda ke da burin kaiwa kwallaye 1,000, ya zira kwallaye 99 a cikin wasanni 111 da ya buga tun bayan zuwansa Al Nassr, inda ya kawo yanzu ya ci kwallaye 938 jimilla a tarihinsa na tamaula

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

Haka kuma wasu ƙungiyoyi a Turai sun nuna sha’awar ɗaukar ɗan wasan.

Majiyoyi sun bayyana cewa Brentford na son a ce darajar Mbeumo ta kai irin kuɗin da United ta biya wajen ɗauko Cunha kafin su yarda su sayar da shi.

Mbeumo ya zura ƙwallaye 20 a kakar wasan da ta gabata, kuma ya taimaka aka zura wasu tara.

Sai dai akwai yiwuwar shi da abokin wasansa na tawagar Kamaru, Andre Onana, ba za su buga wasannin farko na sabuwar kakar wasa ba saboda za su wakilci Kamaru a gasar cin kofin ƙasashen Afirka da za a buga a Maroko.

Kamaru za ta fara buga wasa da Gabon ranar 24 ga watan Disamban 2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • ’Yan sanda sun kashe ‘yan fashi da ƙwato makamai a Kaduna
  • Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
  • MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne
  • ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi 2, sun kama wasu a Kaduna
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6
  • Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford