Ronaldo ya tsawaita kwantaraginsa a Al Nassr
Published: 27th, June 2025 GMT
Cristiano Ronaldo ya sanya hannu kan yarjejeniyar tsawaita kwatiraginsa da shekara biyu a ƙungiyar Al Nassr da ke buga gasar Saudi Pro League.
Wannan dai na nufin kyaftin din na tawagar Portugal zai ci gaba da zama a ƙungiyar har 2027, lokacin da zai kai shekara 42 a duniya.
Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun IslamiyyaAl-Nassr ta bai wa Ronaldo kwantiragi mafi tsada a tarihin wasanni, inda ya rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fam miliyan 24.
Ɗan wasan mai shekara 40 ya je Al Nassr ne a Disamban 2022, bayan raba gari da Manchester United.
A ƙarshen watan Yunin da muke ciki ne kwantiraginsa na farko zai ƙare a ƙungiyar da ke Saudiyya.
Bayan sanya hannun ɗan wasan wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar ya ce “An buɗe sabon babin buri da sha’awar ci gaba da kafa tarihi tare” a shafinsa na Instagram.
Duk da cika shekaru 40, Ronaldo ya ci gaba da taka rawar gani, inda a kakar wasan da ta gabata ya zura kwallaye 35 a wasanni 41 da ya buga a duk gasa, lamarin da ya ba shi damar karewa a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar Saudi Pro League a shekaru biyu ke nan a jere.
Ronaldo wanda ke da burin kaiwa kwallaye 1,000, ya zira kwallaye 99 a cikin wasanni 111 da ya buga tun bayan zuwansa Al Nassr, inda ya kawo yanzu ya ci kwallaye 938 jimilla a tarihinsa na tamaula
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Haka kuma wasu ƙungiyoyi a Turai sun nuna sha’awar ɗaukar ɗan wasan.
Majiyoyi sun bayyana cewa Brentford na son a ce darajar Mbeumo ta kai irin kuɗin da United ta biya wajen ɗauko Cunha kafin su yarda su sayar da shi.
Mbeumo ya zura ƙwallaye 20 a kakar wasan da ta gabata, kuma ya taimaka aka zura wasu tara.
Sai dai akwai yiwuwar shi da abokin wasansa na tawagar Kamaru, Andre Onana, ba za su buga wasannin farko na sabuwar kakar wasa ba saboda za su wakilci Kamaru a gasar cin kofin ƙasashen Afirka da za a buga a Maroko.
Kamaru za ta fara buga wasa da Gabon ranar 24 ga watan Disamban 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp