Ronaldo ya tsawaita kwantaraginsa a Al Nassr
Published: 27th, June 2025 GMT
Cristiano Ronaldo ya sanya hannu kan yarjejeniyar tsawaita kwatiraginsa da shekara biyu a ƙungiyar Al Nassr da ke buga gasar Saudi Pro League.
Wannan dai na nufin kyaftin din na tawagar Portugal zai ci gaba da zama a ƙungiyar har 2027, lokacin da zai kai shekara 42 a duniya.
Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun IslamiyyaAl-Nassr ta bai wa Ronaldo kwantiragi mafi tsada a tarihin wasanni, inda ya rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fam miliyan 24.
Ɗan wasan mai shekara 40 ya je Al Nassr ne a Disamban 2022, bayan raba gari da Manchester United.
A ƙarshen watan Yunin da muke ciki ne kwantiraginsa na farko zai ƙare a ƙungiyar da ke Saudiyya.
Bayan sanya hannun ɗan wasan wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar ya ce “An buɗe sabon babin buri da sha’awar ci gaba da kafa tarihi tare” a shafinsa na Instagram.
Duk da cika shekaru 40, Ronaldo ya ci gaba da taka rawar gani, inda a kakar wasan da ta gabata ya zura kwallaye 35 a wasanni 41 da ya buga a duk gasa, lamarin da ya ba shi damar karewa a matsayin dan wasan da ya fi zura kwallaye a gasar Saudi Pro League a shekaru biyu ke nan a jere.
Ronaldo wanda ke da burin kaiwa kwallaye 1,000, ya zira kwallaye 99 a cikin wasanni 111 da ya buga tun bayan zuwansa Al Nassr, inda ya kawo yanzu ya ci kwallaye 938 jimilla a tarihinsa na tamaula
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure
Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sadau, ta yi aure da masoyinta, Ibrahim Garba.
An ɗaura auren a ranar Asabar a Masallacin da ke Unguwan Rimi, a Jihar Kaduna, bayan Ibrahim ya biya sadaki Naira 300,000.
Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfaraRahama, ta sanar da ɗaurin auren a shafinta na Facebook, inda ta gode wa Allah tare da neman addu’a daga masoyanta.
Ta bayyana farin ciki da godiyarta, tare da fatan wannan sabon babi na rayuwarta zai kasance mai albarka.
Auren mata na zuwa ne watanni biyu bayan rasuwar mahaifinta, Ibrahim Sadau.
’Yan uwanta sun yaɗa hotuna da bidiyon bikin a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama suka yi mamakin yadda aka yi bikin ba tare da sanin jama’a ba.
Rahama, wacce furodusa ce a Kannywood, an naɗa ta memba a Kwamitin Fasaha na shirin Investment in Digital and Creative Enterprise (iDICE).
An ba ta muƙamin ne a 2024 ƙarƙashin ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima.