Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
Published: 26th, June 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga watan Yunin 2025, a matsayin hutun rana daya na sabuwar shekarar musulunci ta 1447.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da ofishin shugaban ma’aikatan Kano ya fitar a yammacin wannan Larabar.
Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya Arsenal za ta ɗauki ɗan ƙwallon Brentford Christian NorgaardSanarwar wadda babban sakatare a ofishin shugaban ma’aikatan, Ashiru Abdullahi ya fitar, ta bukaci ma’aikatan jihar da su yi amfani da wannan dama domin yi wa jihar da kuma kasa baki ɗaya addu’ar zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.
Aminiya ta ruwaito Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, a jiya Talata yana ba da umarnin fara duban watan Muharram na sabuwar shekarar musulunci ta 1447 daga yau Laraba, 29 ga watan Zulhijjan 1446.
Kawo yanzu Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Islama da Sarkin Musulmin ke jagoranta ba ta sanar da ganin jinjirin watan na Muharram ba.
Sai dai kuma a yau din aka samu rahoton ganin watan sabuwar shekarar musulunci ta 1447 Bayan Hijira a Saudiyya.
Cikin wani saƙo da shafin Haramain na Saudiyya ya wallafa ya ce an ga watan da maraicen yau Laraba, 25 ga watan Yuni.
Hakan na nufin shekarar 1446 ta zo ƙarshe wannan rana a ƙasar ta Saudiyya, inda goben za ta kasance 1 ga Muharamm, watan farko a kalandar musulunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano Muharram Sabuwar shekara sabuwar shekarar musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
“Kuma za a yi hakan ne saboda a matsayinmu na al’umma, muna ci gaba da ƙoƙarin canza abubuwan da ‘yan siyasa ba sa son canzawa,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa ba yau aka fara aikin gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar kan batun cin gashin kan ƙananan hukumomi ba.
Ejah ya ƙara da cewa ana sa ran kashi biyu cikin uku na ‘yan majalisar wakilai za su kaɗa ƙuri’ar amincewa ko kuma ƙin amincewa da gyaran.
Ya ƙara da cewa gwamnatin Bola Tinubu ta bayar da umarnin ne kawai, biyo bayan hukuncin da kotun ƙoli ta yanke, cewa a biya kason kuɗaɗen da majalisun za su samu kai tsaye a asusunsu.
A cewarsa, wannan ba gyara ba ne, domin kuwa sai an zagaya jihohi 36 yadda al’umma za su mara masa baya kafin ya zama doka.
“Abin da muka yi shi ne yunƙurin zartarwa na ganin ƙananan hukumomi sun samu kuɗaɗensu kai tsaye amma hakan ba zai yi tasiri ba saboda tanade-tanaden hukuncin kotun ƙoli bai wuce tsarin mulki ba,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp