Aminiya:
2025-06-27@13:26:34 GMT

NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 

Published: 27th, June 2025 GMT

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta  kafa karamar cibiyar kula da muggan kwayoyi a Damaturu babban birnin jihar Yobe.

Kwamandan hukumar a Jihar, Abdulazeez Ogunboye  ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Damaturu a wani bangare na bikin ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya ta shekarar 2025.

Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya

Ogungboye ya kara da cewa cibiyar wacce tun daga lokacin da ta fara aiki na daya daga cikin nasarorin da hukumar ta samu a jihar.

“An shigar da mutane tara da suke ta’ammali da muggan kwayoyi a cibiyar, daga cikin su an samu nasarar gyara halayyar mutum takwas halayyar su, an sallame su tare da sake haduwa da iyalansu, yayin da daya ke ci gaba da karbar hoton gyaran hali.

“Daya daga cikinsu yanzu haka ya samu tallafin fara gudanar da harkokin kasuwanci don dogaro da kai tare da watsar da waccar mummunar dabi’a ta ta’ammali da muggan kwayoyi,” in ji Ogunboye.

Kwamandan ya ce bisa la’akari da tsadar ayyuka a cibiyar, hukumar ta hada kai da masu hannu da shuni a jihar domin taimaka wa a wannan kokarin gyaran halim masu ta’ammali da kwayoyin.

Kwamandan ya kuma shawarci masu shaye-shaye a kananan hukumomi 17 na jihar da su tuntubi kwamandojin shiyya na hukumar da ke kusa da su kan yadda za su shiga wurin, wanda ya ce shi ne irinsa na farko a tarihin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Miyagun Kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.

 

Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su.
Sai dai a wannan zamani ‘yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikin su ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita.
Ko wadanne matakai ya kamata ‘yan Najeriya su ringa dauka wajen kare kan su da ma lafiyar jikin su?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A YAU na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda ‘yan Najeriya zasu dinga kula da lafiyar jikin su.

Domin sauke shirn, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
  • Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
  • Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya