NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe
Published: 27th, June 2025 GMT
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kafa karamar cibiyar kula da muggan kwayoyi a Damaturu babban birnin jihar Yobe.
Kwamandan hukumar a Jihar, Abdulazeez Ogunboye ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Damaturu a wani bangare na bikin ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya ta shekarar 2025.
Ogungboye ya kara da cewa cibiyar wacce tun daga lokacin da ta fara aiki na daya daga cikin nasarorin da hukumar ta samu a jihar.
“An shigar da mutane tara da suke ta’ammali da muggan kwayoyi a cibiyar, daga cikin su an samu nasarar gyara halayyar mutum takwas halayyar su, an sallame su tare da sake haduwa da iyalansu, yayin da daya ke ci gaba da karbar hoton gyaran hali.
“Daya daga cikinsu yanzu haka ya samu tallafin fara gudanar da harkokin kasuwanci don dogaro da kai tare da watsar da waccar mummunar dabi’a ta ta’ammali da muggan kwayoyi,” in ji Ogunboye.
Kwamandan ya ce bisa la’akari da tsadar ayyuka a cibiyar, hukumar ta hada kai da masu hannu da shuni a jihar domin taimaka wa a wannan kokarin gyaran halim masu ta’ammali da kwayoyin.
Kwamandan ya kuma shawarci masu shaye-shaye a kananan hukumomi 17 na jihar da su tuntubi kwamandojin shiyya na hukumar da ke kusa da su kan yadda za su shiga wurin, wanda ya ce shi ne irinsa na farko a tarihin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Miyagun Kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo
Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun kai samame a Ɗakin Karatun Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, a Jihar Ogun, inda suka kama wasu matasa da ake zargin ’yan damfara ne.
Samamen ya faru ne da safiyar ranar Lahadi a sashen otal na ɗakin karatun.
’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a ChadiGidan Obasanjo na musamman yana cikin harabar ɗakin karatun.
Wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, ya nuna yadda wasu matasa ke gudu domin ka da EFCC ta kama su.
Rahotanni sun ce jami’an EFCC sun ƙwace sama da motoci 20 tare da wasu kayayyaki masu daraja.
Wani jami’in EFCC ya shaida wa Aminiya cewa samamen ya samo asali ne daga Ofishin EFCC na Legas.
Daraktan Kamfanin OOPL Ventures, Mista Vitalis Ortese, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa suna ƙoƙarin samun ƙarin bayani daga EFCC.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai yi bincike kafin ya yi wa manema labarai ƙarin bayani.
Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan jami’an EFCC daga Ofishin Ibadan suka kama mutum 56 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a wani otal mai suna K-Hotel da ke Itori, a Jihar Ogun.
An kama ɗaya daga waɗanda ake zargin da bindigogi guda biyu.
EFCC ta kuma ƙwato motoci shida masu tsada, wayoyin salula 89, kwamfutoci, da wasu takardu.
Hukumar ta ce nan ba da jimawa ba za ta gurfanar da dukkanin waɗanda ta kama a gaban kotu.