Leadership News Hausa:
2025-05-19@21:41:58 GMT

Fahimtar Hakikanin kasar Sin

Published: 19th, May 2025 GMT

Fahimtar Hakikanin kasar Sin

Hawa wannan babbar katangar na koyar darussa masu masu ma’ana,- daya daga cikinsu shi ne tsayin daka da ya kai ga Sinawa zuwa ga samun daukaka. Wannan gogewa ta nuna kyakkyawar dabi’ar aikin Sinawa, wanda ya ba da gudummawa ga ci gaban da suka samu a cikin shekaru 40 da suka gabata.

Kafin wannan lokacin, jami’ar Yang Boazhin ya lura cewa, kasar Sin ta fi sauran sassan Afirka talauci.

Ta ba da labarin ziyarar da ta kai Afirka a shekarar 1985 a matsayin jami’ar diflomasiyya, inda ta tabbatar da cewa Afirka na da gagarumin ci gaba a wannan lokacin.

Jamhuriyar kasar Sin, mai yawan al’umma biliyan 1.4, ta kunshi gundumomi hudu da larduna 23, tare da yankuna biyar masu cin gashin kansu da ke wakiltar kabilu daban-daban, da yankuna 21 na musamman na gudanarwa.

Boazhin, jami’ar diflomasiyyar kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin na mutunta ‘yan tsiraru, shi ya sa ba a yi yakin basasa ba. Ta yi nuni da cewa, Hong Kong, a da tana karkashin mulkin Birtaniya, yanzu ta zama yanki na kasuwanci kyauta.

Ta kara da cewa, “Ana kwatanta kasar Sin da Turai domin tana da yawan al’umma wanda ya kai kashi uku bisa uku na Afirka. Muna da iyaka da kasashe makwabta 14, fiye da kowace kasa.

Boazhin ta bayyana cewa, Sarki kin Shi Huang ya hade kasar Sin a shekara ta 221 kafin haihuwar Isa Yesu Almasihu, ko da yake kasar ba ta bin tsarin tarayya. Gwamnatin ta yi juriyar zama na tsawon shekaru 2,000 a karkashin mulkin sarakuna 408 a cikin dauloli 16.

Katafariyar ganuwar ta kasar Sin, wacce a yanzu ta zama wani muhimmin wurin yawon bude ido, an gina ta ne da farko domin samar da tsaro, ba don fadadawa ba. Ta ratsa yankuna 15 kuma ta yi kokarin maido da guda 14 maidowa.

An fara habaka masana’antu na kasar Sin da kirkirar abin fashewa, da wata na’urar kwamfuta mai nuna alkibla, madabba’a, da kuma yin takardu- gudummawar da ta habaka wayewar dan’Adam.

Daular Song, daga karni na 10 zuwa na 13, ta fara bug takardu, yayin da Zheng He, fitaccen shugaba, ya fara binciken teku daga shekarar 1405 zuwa 1433.

Boazhin ta ce, “Ba mu taba bautar da mutane a Afirka ba, ko kuma ba mu kwace kasa ko tilasta wa wani ya koyi harshenmu tun kafin shekarar 1492, kuma muna da iko,” in ji Boazhin, inda ta bayyana tushen dabarun kasar Sin na ketare da ke da muhimmanci a yau.

Duk da karfin arzikin da take da shi a wancan lokacin, kasar Burtaniya ta mamaye kasar Sin a lokacin juyin juya halin masana’antu.

“Yakin Opium, wanda ya fara a shekara ta 1850, ya samo asali ne sakamakon shawarar da kasar Sin ta dauka na kona opium tare da haramta amfani da ita a tsakanin ‘yan kasarmu, wanda ya kai ga mamayewa daga kasashen yammacin Turai. A sakamakon haka, Shanghai ta mamaye, kuma Hong Kong ta fada karkashin ikon Birtaniya, wanda ya raunana al’ummarmu.”

A shekara ta 1911, Yat-sen ya jagoranci wani gagarumin juyin-juya hali wanda ya haifar da jamhuriyya, amma abin ya ci tura, wanda hakan ya ba da damar kafa jam’iyyar kwaminisanci ta kasar Sin a wannan shekarar, wanda daga karshe ya kai ga jagorancin da kasar Sin ke da shi a halin yanzu.

Mao Zedong ya kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, mai jama’ar da yawanta ya kai miliyan 540. A yau, tsarin siyasar kasar Sin ya zama na gurguzu karkashin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (CPC). Jam’iyyar CPC ta shafe shekaru 78 tana mulkin kasar, duk da cewa akwai wasu jam’iyyun siyasa guda takwas da ke ba da ra’ayi sabanin ra’ayi da ya dace da muradun kasa.

A shekarar 1953, kasar Sin ta gina cibiyar masana’antu ta farko ta kasa, tare da raya aikin gona don tabbatar da samar da abinci ga al’ummarta, har ma ta mayar da kashi 15 cikin 100 na yankunan hamada da tsaunuka zuwa gonaki.

A shekarar 1964, kasar Sin ta yi nasarar gwada bam din atomic da hydrogen.

A shekarar 1970, Deng diaoping ya ba da shawarar yin gyare-gyare don daukaka jama’a ta hanyar sauya tsarin gine-gine.

Shekarar 1978 ta kasance wani muhimmin lokaci ga jama’ar kasar Sin, wanda ya haifar da juyin juya halin al’adu, lokacin da kudin shigar kowane dan kasar Sin ya kai Dalar Amurka 156 kacal.

kasar Sin ta yi tsari na sauye-sauyen yankunan karkara, inda ta bai wa manoma damar ci gaba da kasancewa a cikin al’ummominsu, wasu daga cikinsu an yi musu lakabi da Hero Bay billage. An biya wa manoma diyya na zamansu, an ba su fili, an kuma ba da tallafi daban-daban.

A wannan lokaci, gwamnati ta kara farashin sayen hatsi, ta yadda za a rage yunwa. Sinawa suna alfahari da saukaka musu talauci.

Mallakar motoci masu zaman kansu ba abin damuwa ba ne ga mutane da yawa, saboda gyare-gyare a fannin sufuri ya hada dukkanin al’ummomi, kauyuka, da garuruwa ta hanyoyi daban-daban na jirgin kasa, motocin bas, hanyar intanet, samar da wutar lantarki, da wadata gari da haske.

Wadannan ci gaban da aka samu sun bude tattalin arzikin kasar Sin ga duniya, tun daga yankunan gabar tekun Hong Kong, wadanda suka jawo jarin kasar waje.

An kafa yankuna hudu na musamman na tattalin arziki, ciki har da Shenzhen, wani karamin kauye kusa da Hong Kong, yanzu cibiyar masana’antu. Shenzhen tana da yawan jama’a miliyan 18 da ma’aunin kudi na jimillar lasuwancin da aka samar wato (GDP) na Dala tiriliyan 3.68, wanda ya sanya ta a matsayin birni na 11 mafi girma a duniya.

Kasar Sin ta kafa tsarin tattalin arzikinta na gurguzu a shekarar 1992, sannan ta shiga kungiyar WTO a shekarar 2001, tare da saukaka kasancewar kayayyakin kasar Sin a duniya.

Shekaru 40 na yin gyare-gyaren da aka yi a baya sun inganta tattalin arzikin kasar Sin sosai, tare da samun jari daga kamfanoni 450 na duniya.

bangaren kera motoci na kasar Sin ya samu bunkasuwa mai saurin gaske, yana sa kaimi ga mazauna birane.

kasar Sin ita ce babbar kasa a fannin fasaha, bayan da ta aiwatar da tsarin GPS a shekarar 2021.

A shekarar 2024, an samar da robobin masana’antu sama da 500,000 a kasar Sin, yayin da majalisar wakilan kasar Sin ta kafa manyan manufofi.

Jama’ar kasar Sin yanzu suna more tsawon rai saboda ingantaccen tsarin kiwon lafiya. Gwamnati tana ba da kulawa ta musamman ga yara, karancin mace-mace, da ayyukan sadaukarwa ga manyan ‘yan kasa, wadanda ba sa biyan kudin ayyukan jin dadi, gami da tallafin abinci.

Ilimi dole ne ga yara har zuwa shekaru tara, kuma akwai dabarun kasa don horar da mutane masu hazaka, tare da jami’o’i da kwalejoji kusan 3,200 suna daukar adadi masu shiga kashi 99.9 cikin dari.

Yunkurin da kasar Sin ta yi na rage fitar da iskar ‘Carbon’ ya sa aka mai da hankali kan kera motocin lantarki da masu amfani da makamashi mai tsafta, kamar iska da hasken rana.

kasar Sin tana tafiyar da tsarin tattalin arziki na dijital. A baya, jinkirin biyan haraji yana haifar da hukunci, amma a yau, ‘yan kasa za su iya biyan haraji ta hanyar amfani da wayoyin hannu da ID a cikin dakika guda, godiya ga samun damar intanet ta samar da miliyan 730 na masu amfani da intanet daga cikin al’umma biliyan 1.4.

Don tabbatar da samar da guraben ayyukan yi ga ‘yan kasar, kasar Sin na samar da guraben ayyukan yi miliyan 15 a duk shekara a dukkan bangarori, inda ta fitar da mutum miliyan 800 daga kangin talauci tsakanin shekarar 1979 zuwa 2020.

Yawan mutanen da suka tsufa, wadanda shekarunsu suka kai 60 zuwa sama, ya kai miliyan 310, wanda ke wakiltar kashi 18 cikin 100 na yawan jama’ar kasa.

Gwamnatin kasar Sin ta nuna rashin amincewa da cin hanci da rashawa, inda jam’iyya mai mulki da ‘yan adawa suka yi biyayya ga wannan ka’ida.

Masana sun yi nuni da cewa, idan kasar Sin da kasashe masu tasowa za su iya yin hadin gwiwa, to duniya za ta zama wuri mafi kyau.

Yayin wani taron kara wa juna sani na shugabannin kungiyoyin ‘yan jarida na kasashe abokan hadin gwiwa a fannin raya rayuwar al’umma, Mr. Wu Hao, mataimakin Daraktan Sashen Gudanarwa na Shirye-shiryen Horar da Kayayyakin Agaji na kasar Sin, ya bayyana cewa, “Za ku ci karo da hakikanin kasar Sin, al’adunta, jama’arta, da da kuma tarihinta.”

Bayan makonni biyu a cikin wannan kasa mai fadi da ban mamaki, hakika mun hadu da mutane, al’adunsu, salon rayuwarsu da tunaninsu. Mun dandana ainihin kasar Sin, kuma na same ta tana da ban sha’awa sosai.

Yayin da Mr Wu ya yi magana game da falsafa, akida, da ayyukan kasar Sin, ya bayyana a fili cewa yin aiki tare don samar da zaman lafiya wata muhimmiyar hanya ce ta ci gaba.

A kan tafiya zuwa zamani kuwa, kamar yadda Wang Yongzhong ya bayyana, wadannan mutane masu ban mamaki sun yi aiki tukuru don cimma irin wannan nasara.

Tun daga ranar farko da na isa kasar Sin, na lura da aikin gina sabbin layukan karkashin kasa na birnin Beijing.

Manufar shugaba di Jinping, da nufin cin gajiyar al’ummomin da ke fama da talauci a duniya, ya sanya kasar Sin a sahun gaba wajen girmamawa, da godiya, daga miliyoyin mutane a fadin Asiya, Oceania, Latin Amurka, Afirka, da Turai.

A yayin wata lacca da Mrs du Zhengyuan ta gabatar, an tattauna batun aiwatar da shirin Belt and Road Initiatibe (BRI). A cikin ‘yan shekarun nan, kasar Sin ta kasance kasa mafi saurin bunkasar tattalin arziki a duniya.

A gaskiya, ziyarar kwanaki uku da na kai Chongking, wata kwarewa ta musamman a cibiyar baje kolin kayayyaki ta kasa da kasa ta Chongking, kauyen Hero Bay, tare da tarurrukan da suka dace a rukunin kafofin watsa labaru na Chongking da cibiyar sadarwar kasa da kasa ta yammacin kasar Sin, ta nuna cewa kasar Sin na da kwarin gwiwar cimma nasarori a shekaru masu zuwa!

wannan babban aikin saka hannun jari na kayayyakin more rayuwa yana da nufin habaka hadin kai, kasuwanci, da sadarwa a cikin Eurasia, Latin Amurka, da Afirka.

kasar Sin tana goyon bayan gina tashoshin jiragen sama, tashoshin jiragen ruwa, na’urorin samar da wutar lantarki, gadoji, layin dogo, tituna, da hanyoyin sadarwar, tare da kokarin inganta dangantakar tattalin arziki da hadin gwiwa. Sakamakon wannan shiri dai al’ummar kasashen da suka ci moriyar wannan Shirin, wata irin baiwa ce ta Ubangiji.

Tun da yake ba zai yiwu a kawo kowa ya shaida ainihin kasar Sin ko kuma nuna sakamako da fa’ida a duniya ba, hujja mafi gamsarwa ta ta’allaka ne a cikin wadannan hujjoji da alkaluma da ba za a iya musantawa ba.

Ziyarar babbar ganuwa ta nuna irin girman da kasar Sin take da shi.

A al’adu da yawa, ana koya wa yara karatu da aiki tukuru don tara dukiya. Sabanin haka, al’adun kasar Sin sun sanya dabi’un da za su karfafa wa yara su koyi fasahohi masu kima don taimakawa wasu, da inganta al’umma, da ba da gudummawa ga ci gaban kasarsu.

Sakamakon wannan tunani da al’adu, jama’ar kasar Sin sun mayar da kasarsu ta asali ta zama kasa mai wadata.

Wani dan gajeren fim da farfesa Zhang Long ya gabatar, wanda ke baje kolin masu aikin sa kai wadanda suka yi aiki tukuru don mayar da hamadar Mu Us zuwa koriyar aljanna.

Nasarorin da kasar Sin ta samu, da shirin samar da hanya mai inganci, da gudummawar da take bayarwa ga kasashe da al’ummomi masu fama da talauci, da saurin bunkasuwar tattalin arzikinta, da al’adu da wayewar da take da su, darasi ne da ya kamata ‘yan Nijeriya da ‘yan Afirka su amince da su idan ana son ci gaba.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jama ar kasar Sin tattalin arziki da kasar Sin ta ta kasar Sin jama ar kasa kasar Sin na kasar Sin ya kasar Sin a

এছাড়াও পড়ুন:

Sojan Lebanon Daya Ya Jikkata Sanadiyyar Harin Sojan HKI Da Jirgin Sama Maras Matuki

Jiragen na sojojin HKI sun kai hari ne dai a yau Lahadi a kan hanyar da ta raba tsakanin garin Beit-Yahun da Bent-Jubail dake kudancin kasar.

A garin Kafar-kalla ma wani jirgin saman marar matuki ya jefa bama-bamai masu sauti a kusa da wani gida da dama an rushe shi.

Harin na sojojin HKI yana cikin ci gaba da keta hurumin kasar Lebanon da take yi wanda ya wuce 2000 tun daga tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Nuwamba na 2024.

 Bugu da kari HKI ta girke sojojinta a cikin wasu wurare 5 dake kan iyaka,wanda shi ma keta karjejeniya ce.

Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hizbullah ta sha yin kira ga gwamnatin kasar da ta yi duk abinda za ta iya domin yin matsin lamba domin fitar da ‘yan sahayoniyar daga cikin kasar.

Kungiyar ta Hizbullah ta ja nanata cewa ba za ci gaba da zuba idanu tana Kallon HKI tana keta hurumin kasar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin  
  • Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024
  • Sojan Lebanon Daya Ya Jikkata Sanadiyyar Harin Sojan HKI Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024
  • An Ziyarci Gidajen Tarihin Kasar Sin Sau Biliyan 1.49 A Shekarar 2024
  • Gidauniyar Mangal Ta Dauki Nauyin Yi Wa Mutum 12,300 Masu Cutar Kaba Aiki A Katsina
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce Ba Ta Tsoron Duk Wata Barazana Don Neman Tauyaye Mata Hakki
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya