Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa
Published: 4th, July 2025 GMT
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta umarci Majalisar Dattawa da ta mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya.
A watan Maris, Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha na tsawon watanni shida, bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakaninta da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.
Taƙaddamar ta samo asali ne kan yadda aka canja tsarin zama a zauren majalisar.
Bayan dakatarwar, Natasha ta zargi Akpabio da yunƙurin cin zarafinta, inda ta kai ƙara Majalisar Ɗinkin Duniya kan lamarin.
A ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta yanke hukunci cewa dakatarwar watanni shida da aka yi wa Natasha ta yi tsanani.
Ta ce dokar da Majalisar Dattawa ta dogara da ita ba ta fayyace adadin kwanakin da za a iya dakatar da ɗan majalisa ba.
Alƙalin kotun ta ƙara da cewa, tun da ‘yan majalisa ke da kwanaki 181 kacal da suke zama a kowane zangon mulki, dakatar da ɗan majalisa tsawon wannan lokaci na nufin mutane daga yankinsa ba za su samu wakilci ba.
Mai shari’a Nyako ta ce ko da yake Majalisar Dattawa na da ikon hukunta mambobinta, amma hakan bai kamata ya kai ha hana al’umma samun wakilcinsu ba.
Don haka kotun ta umarci Majalisar Dattawa ta mayar da Natasha bakin aikinta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Binta Nyako dakatarwa Majalisar Dattawa umarni Majalisar Dattawa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA