A ranar Litinin, Ratcliffe ya shaida wa BBC cewa wasu daga cikin ‘yan wasan Manchester United ba su da ƙwarewa, amma ana biyansu albashi mai yawa fiye da yadda ya dace.

Ya kuma bayyana shirin gina sabon filin wasa mai tsadar Yuro biliyan 2, wanda zai iya ɗaukar mutum 100,000 idan aka kammala.

A ‘yan kwanakin nan, magoya bayan Manchester United sun ci gaba da nuna fushinsu kan iyalan Glazer, masu mallakar sama da kashi 70 na kulob ɗin.

Har ila yau, Ratcliffe bai samu cikakken goyon baya daga ma’aikatan ƙungiyar ba tun bayan zuwansa a shekarar da ta gabata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙungiya ƙwallo Radcliffe

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani fasto da matarsa da mabiyansa a yayin da suke tsaka da ibada a coci da ke a  Jihar Kogi.

Wani ganau da ke cikin cocin a lokacin da aka kai harin, Adegboyega Ogun, ya ce misalin ƙarfe 9.30 na safe ’yan bindigar suka kai harin suna bude wuta.

“Mutane sun qarshe ta ko’ina, har da faston, wanda aka fi sani da Baba Orlando da matarsa da wasu masu ibada duk an yi garkuwa da su. Gaskiya harin ya yi muni, dukkanmu tserewa muka yi daga cocin.”

Sace masu ibadar a ranar Lahadi a Cocin Cherubim and Seraphim ya auku ne bayan a kwanan nan Gwamna Usman Ododo, ya koka da cewa wasu  manyan jagororin ’yan bindiga sun dawo jihar.

Kafin nan a ranar Asabar ’yan bindiga sun tare hanya, suka yi garkuwa da matafiya cikin motoci uku a kan hanyar Isanlu-MakutuIdofin da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Gabas.

Wani mazaunin yankin, Enimola Daramola ya bayyana cewa, “mutum ɗaya ne kacal ya samu tserewa a motocin da aka tafi da su cikin daji.”

“Amma mun samu labari yau cewa sojoji da ’yan banga sun bi sawun ’yan bindigar inda suka yi musayar wuta suka ceto wasu daga cikin mutanen,”

A ranar Lahadi kuma aka samu rahoton cewa an kai wa wata motar haya hari.

“Matuƙin motar da fasinjojin sun tsallake rijiya da baya. Yanzu hanyar ta zama mai hatsari sosai,” in ji David Juwon, mazaunin yankin Isanlu.

Sabon harin Cocin Cherubim and Seraphim na zuwa ne makonni kaɗan bayan makarancinsa da ’yan bindiga suka sace mutane 38 a wani Cocin CAC da ke yankin Eruku na Karamar Hukumar Ekiti a Jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya
  • AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji