A ranar Litinin, Ratcliffe ya shaida wa BBC cewa wasu daga cikin ‘yan wasan Manchester United ba su da ƙwarewa, amma ana biyansu albashi mai yawa fiye da yadda ya dace.

Ya kuma bayyana shirin gina sabon filin wasa mai tsadar Yuro biliyan 2, wanda zai iya ɗaukar mutum 100,000 idan aka kammala.

A ‘yan kwanakin nan, magoya bayan Manchester United sun ci gaba da nuna fushinsu kan iyalan Glazer, masu mallakar sama da kashi 70 na kulob ɗin.

Har ila yau, Ratcliffe bai samu cikakken goyon baya daga ma’aikatan ƙungiyar ba tun bayan zuwansa a shekarar da ta gabata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙungiya ƙwallo Radcliffe

এছাড়াও পড়ুন:

Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yaba da gagarumin cigaba a harkar noma da Gwamna Umar Namadi ya samar cikin shekaru biyu kacal na mulkinsa.

Ya bayyana haka ne a masarautar Gumel cikin Jihar Jigawa, yayin kaddamar da sabon masallacin Juma’a da Gidauniyar Kashim Shettima ta gina a matsayin wani ɓangare na bikin zagayowar cikar Sarkin Gumel shekaru 45 a kan karaga.

A cewarsa, abin sha’awa ne yadda Gwamna Umar Namadi ya mayar da harkar noma a jihar Jigawa zuwa ta zamani cikin shekaru biyu kacal.

Ya jinjina wa Gwamnan da al’ummar Jihar Jigawa bisa wannan ci gaba mai armashi.

Kashim Shettima ya kara taya Sarkin Gumel, Alhaji Muhammadu Sani, murnar cika shekaru 45 a matsayin Sarkin Gumel, tare da yi masa fatan alkhairi.

Ya tabbatar da ci gaba da jajircewar Gidauniyar Kashim Shettima wajen inganta rayuwar ‘yan Najeriya.

A jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa kaddamar dadMasallacin.

Ya kuma taya Sarkin Gumel murnar cika shekaru 45 a kan karaga, tare da yi masa fatan alheri.

Shi ma a nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jinjina wa Mataimakin Shugaban Kasa bisa gina Masallacin Juma’ar.

Namadi ya kuma yaba da jinjinar da VP ya yi kan sauyin da aka samu a harkar noma ta Jigawa, yana mai alkawarin cewa za a cigaba da kara himma a bangaren noma da ma dukkan ababen da za su ciyar da jihar gaba.

Gwamnan ya kara jinjina wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi  da sauran manyan baki bisa halartar taro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa