A ranar Litinin, Ratcliffe ya shaida wa BBC cewa wasu daga cikin ‘yan wasan Manchester United ba su da ƙwarewa, amma ana biyansu albashi mai yawa fiye da yadda ya dace.

Ya kuma bayyana shirin gina sabon filin wasa mai tsadar Yuro biliyan 2, wanda zai iya ɗaukar mutum 100,000 idan aka kammala.

A ‘yan kwanakin nan, magoya bayan Manchester United sun ci gaba da nuna fushinsu kan iyalan Glazer, masu mallakar sama da kashi 70 na kulob ɗin.

Har ila yau, Ratcliffe bai samu cikakken goyon baya daga ma’aikatan ƙungiyar ba tun bayan zuwansa a shekarar da ta gabata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙungiya ƙwallo Radcliffe

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu

Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana kudurinta na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da babban taronta na kasa da aka tsara a yi a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba.

Hakan na zauwa ne duk da sabon umarnin kotun tarayya da ke hana ta ci gaba da shirya taron.

Yadda muka daƙile yunƙurin tsige Akpabio daga shugabancin Majalisa – Orji Kalu DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma

Mataimakin Sakataren Yada Labarai na kasa na jam’iyyar, Ibrahim Abdullahi, ya shaida wa Aminiya cewa hukuncin kotun da ke dakatar da taron “bata lokaci ne kawai,” yana mai jaddada cewa jam’iyyar na bin hukuncin da kotun koli ta yanke a baya wanda ke tabbatar da cewa jam’iyyun siyasa suna da ikon gudanar da harkokinsu na cikin gida ba tare da tsoma bakin kotu ba.

Wannan bayani na Abdullahi ya biyo bayan hukuncin da Mai Shari’a Peter Lifu na Kotun Tarayya da ke Abuja ya yanke a ranar Talata, inda ya hana PDP gudanar da taronta.

Wannan umarni ya saba da hukuncin da Kotun jihar Oyo ta yanke, wanda ya ba jam’iyyar damar ci gaba da shirin taron, lamarin da wasu masana shari’a suka bayyana a matsayin tufka da warwara.

A martaninsa ranar Talata, Abdullahi ya ce PDP ba za ta sake yarda da “hukuncin da aka samo da gangan” ba, yana mai cewa jam’iyyar PDP ‘yan Najeriya ne suka kafa, ba kotu ba.

“Hukuncin bata lokaci ne. Mun yi nisa sosai da ba za a iya dakatar da mu ba,” in ji shi.

“Ba kotu ce ta kafa mu ba, ‘yan Najeriya ne suka kafa mu, kuma su ne ya kamata mu saurara, ba hukuncin da aka samo da gangan ba.

“Ba za su iya dakatar da mu ba. Muna da hukuncin kotun koli da ke cewa harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa suna karkashin ikon su ne kawai, kuma muna bin wannan doka. Ko da wani ya yi watsi da hukuncin Kotun Jihar Oyo da ta ba mu damar ci gaba, ba zai iya watsi da hukuncin kotun koli ba. Ba za mu ci gaba da bin sabanin hukuncin kotuna ba. Mun yi nisa sosai; ba za a dakatar da mu ba.

“Su jira sai bayan mun kammala, sai su gwada kin amincewa da shi, idan za su iya. Duk da haka, suna da damar daukaka kara, amma mu mun yi gaba,” in ji shi.

A gefe guda kuma, tuni mambobin Kwamitin Shirya Babban Taron Kasa na PDP (NCOC) sun kai ziyara Ibadan a ranar Talata domin duba wurin da za a gudanar da taron.

Mataimakin Gwamnan Jihar Oyo, Barista Bayo Lawal, wanda ke shugabantar kwamitin wurin taron na Babban Taron PDP na 2025, ne ya jagoranci duba wurin a Filin Wasa na Lekan Salami.

Kwamitin ya kuma gudanar da taro da masu kula da filin wasan da ‘yan kwangila domin kammala shirye-shiryen kayan aiki kafin taron da ake sa ran yi a ranar Asabar mai zuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci
  • Troost-Ekong ya gargaɗi Super Eagles kan wasan da za ta fafata da Gabon
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno
  • An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
  • Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata