Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan
Published: 15th, March 2025 GMT
A bangaren yawon bude ido kuwa, Ringo Lee, shugaban kungiyar masu shirya tafiye-tafiye, ya koka cewa, hukumomin jam’iyyar DPP na nuna wariya ga wadanda ke son hulda da babban yankin kasar Sin, kuma tilas hakan zai yi mummunan tasiri kan mu’amala ta yau da kullum dake tsakanin bangarorin biyu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 tare da yin garkuwa da wasu 64 a ranar Asabar a Karamar Hukumar Tsafe ya Jihar Zamfara.
Cikin waɗanda ’yan ta’addan suka kashe har da wani jigon jam’iyyar APC, Hon. Umaru Moriki wanda aka bindige a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe, waɗanda aka yi garkuwa da su kuma har da mata da ƙananan yara a kauyen Fegin Baza.
Harin ta faru ne washegarin da Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya ziyarci jihar, inda ya sanar cewa Hedikwata Tsaro ta girke ƙarin jami’an tsaro a jihar.
A yayin ziyarar ministan ya bayyana cewa zai gana da jami’an tsaro inda zai ba su umarni kar su raha wa ’yan ta’adda.
NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh GumiMinistan ya kuma zargi gwamnatin jihar kan abin da yake yi da kuɗaɗen da take samu daga Gwamnatin Tarayya.
Jihar, wadda ita ce mahaifar Matawalle, tana fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga da suka hana ayyukan noma da sauran harkokin tattalin arziki.
Hare-haren bayan nan, kari ne a kan wasu da dama da suka addabi jihar, duk da ayyukan soji da dama domin daƙile matsalar.
Yadda abin ya faruRahotanni sun ce ’yan bindiga kusan 30 ne suka buɗe wuta kan motar Hon. Moriki yayin da yake kan hanyarsa zuwa Kaduna, inda suka kashe shi nan take.
Bayan haka, sun yi garkuwa da mazauna kauyen 64, suka tafi da su zuwa wani wurin da ba a sani ba.
Hon. Moriki, wanda ya taɓa tsayawa takarar kujerar Majalisar wakilai a Mazaɓar Zurmi/Shinkafi, shi ne Sarkin Fada na Moriki a halin yanzu.
Ɗan marigayin, Abubakar Umar Moriki, ɗalibi a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce: “Baba ya yi ƙoƙarin yin u-turn bayan ya lura da ’yan bindiga, amma suka buɗe masa wuta. An harbe shi, ya rasu nan take. An yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci. Allah Ya gafarta masa, ya kuma sanya shi da Aljanna Firdaus.”
An gudanar da sallar jana’izar marigayi a Masallacin Juma’a na Federal Low-cost, Tudun Wada da ke Gusau, ƙarƙashin jagorancin Imam Alƙali Abdullahi Yakubu.
Ministan Tsaron Ƙasa, Alhaji Bello Mohammed Matawalle, ya halarci jana’izar tare da yin ta’aziyya ga iyalan marigayin.
Matawalle ya bayyana rasuwar Hon. Moriki a matsayin babban rashi ga jihar da ƙasa baki ɗaya, la’akari da ayyukan alheri da ya yi wa jama’a, musamman maƙwabta da ’yan uwa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun APC na jihar, Yusuf Idris, ya fitar, Matawalle ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da Aljanna Firdaus, ya kuma ba iyalansa ƙarfin zuciya wajen jure wannan rashi.
Ministan ya bayar da gudummawar Naira miliyan 10, buhunan shinkafa 50, buhunan masara 25 da buhunan gero 25 ga iyalan marigayin, tare da tabbatar musu da kulawa daga gwamnati.
A madadin iyalan marigayin, Ambassador Abubakar Hussaini Moriki ya gode wa ministan bisa kulawa da tausayi da ya nuna.
Ya ce sun san cewa ministan ya soke dukkan ayyukansa na yau domin halartar jana’izar, ya kuma yi tafiya daga garin Maradun zuwa Gusau don yin ta’aziyya da su a wannan lokaci na jarrabawa.