Leadership News Hausa:
2025-11-17@08:29:31 GMT

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

Published: 15th, March 2025 GMT

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

A bangaren yawon bude ido kuwa, Ringo Lee, shugaban kungiyar masu shirya tafiye-tafiye, ya koka cewa, hukumomin jam’iyyar DPP na nuna wariya ga wadanda ke son hulda da babban yankin kasar Sin, kuma tilas hakan zai yi mummunan tasiri kan mu’amala ta yau da kullum dake tsakanin bangarorin biyu. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare.

Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara

’Yan bindiga sun kashe mutum 3 tare da yin garkuwa da wasu 64 a ranar Asabar a Karamar Hukumar Tsafe ya Jihar Zamfara.

Cikin waɗanda ’yan ta’addan suka kashe har da wani jigon jam’iyyar APC, Hon. Umaru Moriki wanda aka bindige a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe, waɗanda aka yi garkuwa da su kuma har da mata da ƙananan yara a kauyen Fegin Baza.

Harin ta faru ne washegarin da Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya ziyarci jihar, inda ya sanar cewa Hedikwata Tsaro ta girke ƙarin jami’an tsaro a jihar.

A yayin ziyarar ministan ya bayyana cewa zai gana da jami’an tsaro inda zai ba su umarni kar su raha wa ’yan ta’adda.

NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi

Ministan ya kuma zargi gwamnatin jihar kan abin da yake yi da kuɗaɗen da take samu daga Gwamnatin Tarayya.

Jihar, wadda ita ce mahaifar Matawalle, tana fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga da suka hana ayyukan noma da sauran harkokin tattalin arziki.

Hare-haren bayan nan, kari ne a kan wasu da dama da suka addabi jihar, duk da ayyukan soji da dama domin daƙile matsalar.

Yadda abin ya faru

Rahotanni sun ce ’yan bindiga kusan 30 ne suka buɗe wuta kan motar Hon. Moriki yayin da yake kan hanyarsa zuwa Kaduna, inda suka kashe shi nan take.

Bayan haka, sun yi garkuwa da mazauna kauyen 64, suka tafi da su zuwa wani wurin da ba a sani ba.

Hon. Moriki, wanda ya taɓa tsayawa takarar kujerar Majalisar wakilai a Mazaɓar Zurmi/Shinkafi, shi ne Sarkin Fada na Moriki a halin yanzu.

Ɗan marigayin, Abubakar Umar Moriki, ɗalibi a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “Baba ya yi ƙoƙarin yin u-turn bayan ya lura da ’yan bindiga, amma suka buɗe masa wuta. An harbe shi, ya rasu nan take. An yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci. Allah Ya gafarta masa, ya kuma sanya shi da Aljanna Firdaus.”

An gudanar da sallar jana’izar marigayi a Masallacin Juma’a na Federal Low-cost, Tudun Wada da ke Gusau, ƙarƙashin jagorancin Imam Alƙali Abdullahi Yakubu.

Ministan Tsaron Ƙasa, Alhaji Bello Mohammed Matawalle, ya halarci jana’izar tare da yin ta’aziyya ga iyalan marigayin.

Matawalle ya bayyana rasuwar Hon. Moriki a matsayin babban rashi ga jihar da ƙasa baki ɗaya, la’akari da ayyukan alheri da ya yi wa jama’a, musamman maƙwabta da ’yan uwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun APC na jihar, Yusuf Idris, ya fitar, Matawalle ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da Aljanna Firdaus, ya kuma ba iyalansa ƙarfin zuciya wajen jure wannan rashi.

Ministan ya bayar da gudummawar Naira miliyan 10, buhunan shinkafa 50, buhunan masara 25 da buhunan gero 25 ga iyalan marigayin, tare da tabbatar musu da kulawa daga gwamnati.

A madadin iyalan marigayin, Ambassador Abubakar Hussaini Moriki ya gode wa ministan bisa kulawa da tausayi da ya nuna.

Ya ce sun san cewa ministan ya soke dukkan ayyukansa na yau domin halartar jana’izar, ya kuma yi tafiya daga garin Maradun zuwa Gusau don yin ta’aziyya da su a wannan lokaci na jarrabawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 
  • Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati