Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan
Published: 15th, March 2025 GMT
A bangaren yawon bude ido kuwa, Ringo Lee, shugaban kungiyar masu shirya tafiye-tafiye, ya koka cewa, hukumomin jam’iyyar DPP na nuna wariya ga wadanda ke son hulda da babban yankin kasar Sin, kuma tilas hakan zai yi mummunan tasiri kan mu’amala ta yau da kullum dake tsakanin bangarorin biyu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
Dakarun Sojin Najeriya, sun ceto wasu mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace a Ƙaramar Hukumar Tsanyawa da ke Jihar Kano.
Wannan zuwa ne bayan mazauna Yankamaye Cikin Gari suka sanar da jami’an tsaro cewa ’yan bindiga sun shiga ƙauyensu a daren ranar Juma’a.
’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar AfrikaWannan na cikin wata sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaftin Babatunde Zubairu, ya fitar ranar Lahadi.
Ya ce sojin ƙasa tare da haɗin guiwar sojin sama da ’yan sanda sun garzaya wajen, inda suka yi artabu da ’yan bindigar, sannan suka ceto mutanen da abin ya shafa.
Sai dai Zubairu, ya ce ’yan bindigar sun riga sun kashe wata mata mai shekaru 60 kafin sojoji su isa yankin.
Ya ƙara da cewa bayan harin farko da suka kai, sojojin sun bi sahun ’yan bindigar zuwa yankin Rimaye, inda suka yi musu luguden wuta, wanda hakan ya tilasta musu barin mutanen da suka sace.
Sai dai har yanzu ba a gano inda mutane huɗu da suka sace suke ba.
Bayanai sun nuna cewar bayan ’yan bindigar sun tsere, sun nufi Ƙaramar Hukumar Kankia da ke Jihar Katsina, kuma jami’an tsaro na ci gaba da bibiyarsu.
Kwamandan rundunar, ya yaba da jarumtar sojojin, ya roƙi jama’a da su riƙa bai wa hukumomin tsaro sahihin bayanai a kan lokaci domin kawar da ’yan bindiga a jihar.