Leadership News Hausa:
2025-11-24@08:41:33 GMT

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

Published: 15th, March 2025 GMT

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan

A bangaren yawon bude ido kuwa, Ringo Lee, shugaban kungiyar masu shirya tafiye-tafiye, ya koka cewa, hukumomin jam’iyyar DPP na nuna wariya ga wadanda ke son hulda da babban yankin kasar Sin, kuma tilas hakan zai yi mummunan tasiri kan mu’amala ta yau da kullum dake tsakanin bangarorin biyu. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare.

Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja

Shugaban Cocin Katolika reshen Kontagora, ƙarƙashin ya ce ɗalibai 88 da aka yi zaton sun tsere yayin harin da ’yan ta’adda suka kai a makarantar St Mary Secondary School da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, har yanzu ba a san inda suke ba.

A cewar majiyoyi, iyaye da dama sun garzaya makarantar domin kwashe ’ya’yansu bayan harin, amma ba ba su yaran ba.

A baya  Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindiga sun kutsa cikin makarantar da daddare a ranar Juma’a, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da ma’aikatan makarantar.

Shugaban Cocin Katolika ta Kontagora, Mai Girma Bishop Bulus Dauwa Yohanna, ya sanar ta hannun mai taimaka masa, Daniel Atori, cewa an yi garkuwa da ɗalibai 303, malamai mata huɗu da malamai maza takwas a yayin harin.

Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno

Ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a ɓangaren firamare, da kuma ɗalibai 199 a ɓangaren sakandare.

Bishop ɗin ya ƙaryata zargin da Sakataran Gwamnatin Jihar Neja ya yi cewa gwamnati ko jami’an tsaro sun yi wa makarantar gargaɗi tun kafin harin.

Ya ce, “Mun tambayi Sakataren Ilimi ko ya samu wata takarda daga gwamnati, ya ce babu; ko an ce ya tura mana wata sanarwa, ma babu. Mun tambaye shi ko an sanar da shi a baki, ya ce a’a. To su faɗa wa duniya wa suka bai wa wannan takarda, ko ta wane hanya aka turo ta?

“Mun kuma tambayar Ƙungiyar Makarantu Masu zaman kansu ta Ƙasa, suma ba su samu wata irin sanarwa ba. Suka ce makarantar an rufe ta kuma an sake buɗe ta kwanaki kaɗan da suka gabata — wannan ma ba gaskiya ba ne. Mu masu bin doka ne,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • An rufe duk makarantu a Kebbi
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 160
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara