Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya
Published: 19th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Yana fatan tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshgan ya bayyana cewa: Iran tana fatan tattaunawarta da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya da za ta tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.
A yammacin jiya Lahadi, a gefen taron dandalin tattaunawa na Tehran na shekara ta 2025, a wata ganawa da ministan harkokin wajen masarautar Oman Badar bin Abdullah al-Busaidi, Shugaba Pezeshkian ya yaba da irin kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma irin rawar da gwamnatin Oman take takawa wajen daukar nauyin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Amurka da Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Yana mai cewa: “Suna fatan sakamakon kokari da kuma sahihan manufofin Sultan Haitham bin Tariq, wadannan shawarwarin za su kai ga cimma yarjejeniyar adalci da za ta tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.”
Shugaban na Iran ya jaddada wajabcin kara samun kusanci a tsakanin kasashen musulmi, yana mai cewa “masu kusanci da juna da fadada hadin gwiwarsu, haka nan masu fatan cutar da al’ummar musulmi za su zama masu haifar da sabani da rabuwar kai a tsakaninsu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan
Rahotannin da su ke fitowa daga kasashen biyu sun ce a jiya Asabar an yi musayar wuta a tsakanin masu tsaron kan iyaka, bisa zargin da Islamabad take yi wa Kabul da taimakon kungiyoyi masu dauke da makamai.
A can kasar Afghanistan kuwa majiyar tsaro ta ce ana yi fada da sojojin Pakistan akan iyakokin jahohi 7. Ma’aikatar tsaron Afghanistan ta ce, sun kai wa sojojin Pakistan hari akan iyakar Diyorand a matsayin mayar da martanin ta sama da Pakistan ta kai wa birnin Kabul da jahohin Khust da Nangarhar.
Pakistan tana zargin kungitar Taliban ta kasarta da kai hari daga cikin kasar Afghanistan,lamarin da Kabul take korewa.
Harin da kungiyar Taliban din Pakistan a yankin Kahibar dake kan iyaka, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 23 daga cikinsu da akwai jami’an tsaro 20 da kuma fararen hula 3.
Bayanin rundunar sojan kasar Pakistan y ace; Hare-haren da kungiyar ta Taliban take kai wa sun ci rayukan mutane fiye da 500 daga cikinsu da akwai sojoji 311 da ‘yan sanda 73.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Bayan Yakin Kwanaki 12, Kifar Da Gwamnatin JMI Ya Fita Daga Zabin Makiya: Aref October 11, 2025 Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take October 11, 2025 HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci