HausaTv:
2025-10-15@05:54:52 GMT

Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis

Published: 4th, July 2025 GMT

Gwamnatin kasar Amurka ta dorawa JMI sabbin takunkuman tattalin arziki ta bangaren man fetur a jiya Alhamis, a dai-dai lokacinda take maganar sake farfado tattaunawa da ita.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto  Scott Bessent sakataren kudi na Amurka yana fadar haka ‘Amurka zata ci gaba da gurgunta tattalin arzikin JMI da dukkan hanyoyin samun kudadenta, har sai ta dawo kan muradunta.

Wannan dai yana daga cikin shirin Amurka na takurawa tattalin arzikin kasar Iran har zuwa lokacinda mutanen kasar zasu kasa hakuri su kuma tashi su kifar da gwamnatin JMI daga cikin gida.

Wannan ne takunkuman tattalin arziki na farko wanda gwamnatin Amurkan ta dorawa JMI bayan yakin kwanaki 12 da ita da HKI suka dorawa kasar.

Takunkuman a halin yanzu ta shafi jami’an gwamnati 7 da kuma wani kamfani mai zaman kansa. Wannan dai yana nuna irin tsarin tupka da warwaran da gwamnatin Amurka take kai, tana neman sake farfado da tattaunawa da kuma kara takurawa kasar Iran a dayan bangaren.

Har’ila yau bayan yakin kwanaki 12 yana cewa ya amince China ta ci gaba da sayan man fetur na kasar Iran.

Wannan dais hi ne takunkuman tattalin arziki na 8 kan abinda ya shafi man fetur wanda gwamnatin Amurka ta dorawa Iran tun bayan dawowansa kan white a farkon wannan shekarar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da gwamnatin

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta yi tir da maganganun shugaban kasar Amurka Donal Trump a cikin majalisar dokokin HKI a jiya Litinin inda ya bayyana cewa HKI ta sami nasara a yakin da ta kaiwa JMI a cikin watan Yunin da ya gabata, sannan daga karshe ya ce akwai bukatar a cimma yarjeniya da JMI kan shirinta na makamashin Nukliya.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ma’aikatar na cewa jawabin Trump a majalisar Knesset jawabi ne wanda bai da wani kima. Musamman a lokacinda yake gabatar da ita a gababan yan ta’adda makasa.

Ma’aikatar ta tunatarwa Trump har yanzun tana jirin randa za’a gabatar da shi a gaban kuliya kan kissahn Janar shahida Qasim Sulaimani, wanda shi gwarzon yaki da kungiyoyin yan ta’adda a Iraqi da Siriya. Shi ya jagoranci kawo karshen mamayar da kungiyoyin Daesh suka yiwa kasashen biyu a shekara 2017.

Ma’aikatar da bayyana Amurka a matsayin kasa wacce ta fi ko wace kasa a duniya goyawa yan ta’adda a yankin Asiya da kudu da kuma wasu wurare, sannan tana amfani da kujerar Veto a kwamitin tsaro na MDD don kare yan ta’adda da kuma hanasu gurfana a gaban kuliya don fuskantar adalci.

Ma’aikatar ta yi watsi da maganar Trump kan cewa shirin Iran na makamashin Nukliya ba ta zaman lafiya bane, ta kuma kara da cewa Trunp bai da wata shaida da take tabbatar da hakan, sannan ta kara da cewa, wannan zargin bai yadda zata halatta kaiwa JMI yaki ba.

Daga karshen ma’aikatar ta tabbatar da cewa kwarar makaman Amurka da na kasashen yamma zuwa HKI shi ne yake jawo rashin zaman lafiya a yankin. Kuma matukar HKI tana nan babu kuma zaman lafiya a yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Gagarumar Zanga Zangar Goyon Bayan Falasdinawa A Australia Da Indonasia October 14, 2025 Syria: Busaina Sha’aban Ta Karyata Labaran Da Aka Danganta Ma Ta Na Ganawa Da Jami’an Iraniyawa October 14, 2025 Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya October 14, 2025  MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025 October 14, 2025 Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya October 14, 2025 Larijani:  Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa  Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara October 14, 2025 Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta  Ga Kungiyar Red Cross October 13, 2025 Iran: Kakabawa Kasa Mai Makwabta 16 Takunkumi Ba Abu Ne Mai Sauki Ba. October 13, 2025 An Gano Gawarwaki 323 Karkashin Burabutsai Bayan Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 13, 2025 Tehran Ta yi Gargadi Game Da  Barazanar Yaduwar Fadan Iyakar Afghanisatan Da Pakistan. October 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
  • Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAN
  • Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI
  • Iran: Kakabawa Kasa Mai Makwabta 16 Takunkumi Ba Abu Ne Mai Sauki Ba.
  • Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh
  • Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine
  • Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon
  • Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh