Aminiya:
2025-05-19@12:59:37 GMT

Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5

Published: 19th, May 2025 GMT

Akalla manoma 90 ne mayakan kungiyoyin Boko Haram da ISWAP suka kashe a Jihar Borno cikin watani biyar da suka gabata.

Mayakan kungiyar sun kuma yi garkuwa da wasu da dama baya ga wadanda suka tsallake rijiya da baya a hare-haren kungoyiyoyin da raunin harbi.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa kungiyoyin ‘yan ta’addan sun kai hare-haren ne a tsakanin watan Janairu zuwa Mayun nan da muke cikin na shekarar 2025.

Hari na baya-bayan nan shi ne wanda mayakan kungiyar ISWAP suka yi ritsa manoman da ke aiki a gonakin wake suka yi wa mutum 50 kisan gilla a yankin Karanti da ke Karamar Hukumar Kukawa a ranar Alhamis, 15 ga watan Mayu.

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

A gefe guda kuma, mayakan kungiyar Boko Haram da ba sa ga-maciji da ISWAP sun kai wani hari garin Baga, mai tazarar kilimita 9, inda suka yi wa masunta da manoma kisan gilla.

Wata majiya a garin na Baga ta bayyana cewa kafin harin na Boko Haram manoma da masunta da ke garin sun jima suna samun kariya daga wani shugaban ISWAP a yankin.

Majiyar ta ce, manoman, “suna da takarda daga kwamandan da ke kula da yankin Malam Karanti zuwa Dawashi, mai suna Amir Akilu, kuma sun shafe watanni a karkashin kulawarsa, inda suke biyan haraji, kafin wannan harin.”

Ta bayyana cewa mayakan Boko Haram sun yi amfani da damar tafiyar da kwamandan na ISWAP da mayakansa, wajen kaddamar da mummunan harin, saboda zargin manoman da yi wa abokan gaba leken asiri a kansu.

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya ya bayayana cewa mayakan na Boko Haram sun yi musu kawanya tare da barazanar harbe duk wanda ya yi yunkurin tserewa.

Ya ce, “wasunmu sun ma riga sun fara girbin wakensu kafin aka kawo harin. Suka tara mu a wuri guda suna baraznar kashe duk wanda ya yi yunkurin guduwa, amma duk da haka muka zabi mu tsere maimakon mutuwar wulakanci a hannunsu.

“Ina tabbatar maka sun kashe mutane 50, yawancinsu ta hanyar yankan rago, sa’annan sun yi garkuwa da wadansu. Yanzu haka sun shiga Dawashi suna yin irin wannan kisan gillar,” kamar yadda ya shaida wa wakilinmu bayan ya tsira.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP Kukawa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka

Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bayyana cewa babu wata rubutaciyar shawara data samu daga Amurka.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya musanta ikirarin samun rubutaccen sako daga Amurka kan yarjejeniyar nukiliya.

“Iran ba ta sami wata rubutacciyar shawara daga Amurka ba, kai tsaye ko a kaikaice,” in ji Araghchi a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a.

Wannan matsayi na zuwa ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa Iran ta samu wata shawara daga kasarsa.

Ya kara da cewa sakonnin da muke samu, kamar wanda duniya ke samu, suna cike da rudadi da kace-nace.

Amma matsayin Iran, na daram kuma babu ja da baya, ‘’ ku amince da hakkinmu ku kum akawo karshen takunkumai, idan hakan ya samu to za’a iya cimma matsaya.

Ministan hakokin wajen kasar ta Iran, ya kuma kara da cewa babu wani abu da zai sa Iran ta dakatar da hakkinta na inganta sanadarin uranium na zaman lafiya  ba wanda yake kunshe a cikin ‘yancin da aka baiwa dukkan kasashen da suka sanya hannun kan yarjejeniyar hana yaduwar makamman nukiliya.

A koyaushe muna maraba da tattaunawa bisa mutunta juna, sannan muna watsi da duk wani yunkuri na tilastawa ko matsin lamba. »

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • Wata ‘Yar Jarida Ta Nuna Mamaki Kan Nuna Damuwa Da Ciwon Biden Maimakon Kisan Gillar ‘Yan Sahayoniyya
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
  • ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Borno
  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku