Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5
Published: 19th, May 2025 GMT
Akalla manoma 90 ne mayakan kungiyoyin Boko Haram da ISWAP suka kashe a Jihar Borno cikin watani biyar da suka gabata.
Mayakan kungiyar sun kuma yi garkuwa da wasu da dama baya ga wadanda suka tsallake rijiya da baya a hare-haren kungoyiyoyin da raunin harbi.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa kungiyoyin ‘yan ta’addan sun kai hare-haren ne a tsakanin watan Janairu zuwa Mayun nan da muke cikin na shekarar 2025.
Hari na baya-bayan nan shi ne wanda mayakan kungiyar ISWAP suka yi ritsa manoman da ke aiki a gonakin wake suka yi wa mutum 50 kisan gilla a yankin Karanti da ke Karamar Hukumar Kukawa a ranar Alhamis, 15 ga watan Mayu.
Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?A gefe guda kuma, mayakan kungiyar Boko Haram da ba sa ga-maciji da ISWAP sun kai wani hari garin Baga, mai tazarar kilimita 9, inda suka yi wa masunta da manoma kisan gilla.
Wata majiya a garin na Baga ta bayyana cewa kafin harin na Boko Haram manoma da masunta da ke garin sun jima suna samun kariya daga wani shugaban ISWAP a yankin.
Majiyar ta ce, manoman, “suna da takarda daga kwamandan da ke kula da yankin Malam Karanti zuwa Dawashi, mai suna Amir Akilu, kuma sun shafe watanni a karkashin kulawarsa, inda suke biyan haraji, kafin wannan harin.”
Ta bayyana cewa mayakan Boko Haram sun yi amfani da damar tafiyar da kwamandan na ISWAP da mayakansa, wajen kaddamar da mummunan harin, saboda zargin manoman da yi wa abokan gaba leken asiri a kansu.
Wani wanda ya tsallake rijiya da baya ya bayayana cewa mayakan na Boko Haram sun yi musu kawanya tare da barazanar harbe duk wanda ya yi yunkurin tserewa.
Ya ce, “wasunmu sun ma riga sun fara girbin wakensu kafin aka kawo harin. Suka tara mu a wuri guda suna baraznar kashe duk wanda ya yi yunkurin guduwa, amma duk da haka muka zabi mu tsere maimakon mutuwar wulakanci a hannunsu.
“Ina tabbatar maka sun kashe mutane 50, yawancinsu ta hanyar yankan rago, sa’annan sun yi garkuwa da wadansu. Yanzu haka sun shiga Dawashi suna yin irin wannan kisan gillar,” kamar yadda ya shaida wa wakilinmu bayan ya tsira.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP Kukawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria