Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da labarin da ministan harkokin wajen kasar Jamus ya watsa dangane da shirin Nukliyar kasarsa ya kuma kara da cewa labarin jabu ne.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X . Ya kuma yi watsi da zancen ministan harkokin wajen kasar Jamus wanda yake cewa, jinginar da aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya wato IAEA wanda JMI ta yi,  ya na nuna cewa ba wanda zai bincika ayyukanta na makamashin nukliya ba, kuma ta rufe kofar tattaunawa Kenan.

Aragchi ya bayyana cewa wannan ba haka bane, saboda shirin nukliyar kasar Iran a halin yanzu ya na karkashin majalisar koli ta tsaron kasar Iran ne, don haka ita ce zata fayyece yadda huldar shirin zai kasance tare da hukumar IAEA. Sannan Iran bata fice daga yarjeniyar NPT ba.

Kasar Jamus dai tana goyon bayan hare=hare da HKI da AMurka suka kaiwa JMI a yakin kwanaki 12, dagan  cikin harda hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar. Ya ce aiki ne da bai dace ba wacce JKI ta yi madadin kasashen yamma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar wa al’ummar jihar a shirye ta ke ta ci gaba da kare mutuncin daidaikun mutane da kungiyoyin da suka sadaukar da kansu domin samar musu da sahihin bayanan sirri da za su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijar.

‘Yan sanda a jihar Neja da ma Nijeriya ƙwararru ne don haka za su ci gaba da aiki da kuma nuna basira da ƙwarewa tare da ƙa’idarta ta sirrin rashin bayyana tushen bayanansu don samun sakamako mafi girma.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman wanda ya bayar da wannan tabbacin a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna, ya bayyana cewa a kwanan baya ya halarci wani taron bita da hedkwatar ‘yan sanda ta shirya kan masu bada bayanai wato Informant domin kara kwarewarsa.

Sai dai Adamu Abdullahi Elleman ya danganta raguwar ayyukan aikata laifuka a Minna babban birnin jihar da sahihan bayanai da aka samu daga jama’a, goyon baya daga babban sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun da gwamnatin jihar Neja a karkashin jagorancin Gwamna Umar Bago, da sarakunan gargajiya da kuma matakin da ya dauka na cewa a mafi yawan lokuta yakan shiga sintiri a Minna, wanda DPO da kwamandojin yankin suka goyi bayansa.

A cewarsa sakamakon wannan yunkurin da aka yi da dama daga cikin miyagu da suka tsunduma cikin ayyukan ‘yan daba, an kama su, an kuma gurfanar da su a gaban kuliya, tare da daure su a matsayin misali ga wasu.

Adamu Abdullahi Elleman ya ci gaba da cewa, ya kuma gargadi Hakimai na yankin da su rika taimaka wa miyagu cewa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya manta sabo.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, ya kuma yabawa babbar mai shari’a ta jihar, Mai shari’a Halima Ibrahim bisa goyon bayan da ta bayar wajen ganin an samar da shari’a cikin gaggawa, tare da samun hadin kai tsakanin ‘yan sanda da sauran kungiyoyin tsaro baya ga sabon alkawari da jami’an sa da mazaje suke yi na yakar miyagun laifuka da aikata laifuka a duk lungu da sako na jihar.

Adamu Abdullahi Elleman ya kuma kara da cewa a karkashin sa a matsayinsa na sabon kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja, jin dadin jami’ansa da jami’an rundunarsa shi ne babban abin da ya fi ba da fifiko wajen kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyuka masu inganci.

INT Aliyu Lawal.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
  • Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
  • Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAN
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI
  • Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Aragchi: HKI Ba Zata Mutunta Tsaida Wuta A Gaza Ba
  • Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta
  • Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon