Aminiya:
2025-07-05@17:36:35 GMT

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci 

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin da wani ɗan majalisar Amurka, Chris Smith, ya yi cewa ana tauye wa Kiristoci ’yancin addini a Najeriya.

Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa matsalolin tsaro da ake fuskanta ba su da alaƙa da addini, domin hare-haren ’yan ta’adda na shafar dukkanin Musulmi da Kiristoci.

Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo Wadda ke damfara da sunan matar gwamnan Katsina ta shiga hannu

Tuggar ya ce hare-haren da ake kai wa a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma ba sa ware mabiyan wani addini.

Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwa kan yadda ake yaɗa rahotannin da ba su dace ba, waɗanda ka iya haddasa rarrabuwar kawuna a ƙasar.

Rahoton wata ƙungiya mai suna Open Doors ya ce kashi 89 na Kiristocin da ake kashewa a duniya na faruwa ne a Najeriya.

Sai dai ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta musanta hakan, inda ta ce Musulmi ne ma aka fi kashewa a tashe-tashen hankulan da ake fama da su.

Tun a zamanin mulkin Trump, Amurka ta saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna tauye ’yancin addinin Kiristoci.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta ce wannan batu ba shi da tushe balle makama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matsalar tsaro zargi Gwamnatin Tarayya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu

Baltasar Engonga Ebang, mutumin nan dan kasar Equatorial Guinea da a bara ya saki bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 na fuskantar shari’a a kotu kan badakalar kudade.

Baltasar, wanda tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa ta kasar Equatorial Guinea ne dai an gurfanar da shi a gaban kotu ne bisa zargin karkatar da kudade a karkashin Ma’aikatar Kudin kasar.

Masu shigar da kara na neman a yanke masa hukuncin daurin shekara 18 a kurkuru sannan a umarce shi ya dawo da wasu kudaden masu yawa.

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

Ana dai zarginsa ne da almundahana, azurta kai da kuma rub-da-ciki a kan dukiyar al’umma lokacin da yake rike da mukamin hukumar.

Lauyoyi masu shigar da kara na zargin Baltasar da yin babakere a kan kudi har sama da CFA biliyan daya, kwatankwacin sama da Naira biliyan biyu da rabi.

Bugu da kari, lauyoyin na kuma son a yanke masa hukuncin shekara takwas kan laifin almundahana, shekara hudu da wata biyar kan laifin azurta kai, sai kuma shekara shida kan laifin cin amanar ofishinsa.

Lauyoyin sun kuma bukaci kotun ta ci Baltasar tarar CFA miliyan 910 sannan a haramta masa rike kowanne irin ofishin gwamanti na tsawon lokacin da zai shafe a dauren.

To sai dai lauyoyin wanda ake karar sun yi fatali da dukkan laifukan da ake zargin wanda suke karewa da aikatawa da ma sauran wadanda ake zargin, inda suka ce bas u da tushe.

A watan Disambar bara ne dai bidiyoyin Baltasar na lalata da mata sama da 400 suka cika shafukan sada zumunta. Daga cikin matan da aka gan shi yana lalata da su har da matan ministotin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa
  • Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta