Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci
Published: 15th, March 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin da wani ɗan majalisar Amurka, Chris Smith, ya yi cewa ana tauye wa Kiristoci ’yancin addini a Najeriya.
Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa matsalolin tsaro da ake fuskanta ba su da alaƙa da addini, domin hare-haren ’yan ta’adda na shafar dukkanin Musulmi da Kiristoci.
Tuggar ya ce hare-haren da ake kai wa a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma ba sa ware mabiyan wani addini.
Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwa kan yadda ake yaɗa rahotannin da ba su dace ba, waɗanda ka iya haddasa rarrabuwar kawuna a ƙasar.
Rahoton wata ƙungiya mai suna Open Doors ya ce kashi 89 na Kiristocin da ake kashewa a duniya na faruwa ne a Najeriya.
Sai dai ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta musanta hakan, inda ta ce Musulmi ne ma aka fi kashewa a tashe-tashen hankulan da ake fama da su.
Tun a zamanin mulkin Trump, Amurka ta saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna tauye ’yancin addinin Kiristoci.
Sai dai Gwamnatin Tarayya ta ce wannan batu ba shi da tushe balle makama.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: matsalar tsaro zargi Gwamnatin Tarayya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na shirin sayen jirage marasa matuƙa da wasu kayan aiki domin kare yankunan da ke iyakar Kano da Katsina.
Kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000Gwamna Abba, ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci sansanin rundunar haɗin gwiwa ta JTF, domin ganin yadda suke shirin kare al’umma daga hare-haren ’yan bindiga a yankunan Tsanyawa da Shanono.
Ya roƙi al’ummar yankunan da abin ya shafa da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani game da duk wani motsi na ’yan bindiga.
Gwamnan ya ce ya kai wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ziyara, domin neman taimako kan lamarin, inda shugaban ya amince da buƙatar da aka gabatar masa cikin gaggawa.
Ya umarci dakarun JTF da su yi duk mai yiwuwa wajen ceto mutanen da aka sace a Tsanyawa da Shanono.
“Mun san cewa waɗannan hare-hare sun jawo asarar rayuka, wasu kuma an yi garkuwa da su. Insha Allah za a ceto su,” in ji shi.
Gwamna Abba ya ce sun kai wannan ziyara ne domin fahimtar halin tsaron yankin da kuma ƙarfafa guiwar jami’an tsaro.
Ya ƙara da cewa irin wannan matsalar tsaro sabon abu ne a Kano, amma gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro domin magance ta.
A yayin ziyarar, ya jajanta wa iyalan mutanen da aka sace tare da tabbatar musu cewa gwamnati na ƙoƙarin ganin an dawo da su cikin gaggawa.
Rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 10 aka sace a Tsanyawa da Shanono, ciki har da wata tsohuwa da ’yan bindiga suka hallaka.