HausaTv:
2025-07-04@08:17:48 GMT

Iran : zamu ci gaba da inganta uranium ko da yarjejeniya ko babu

Published: 19th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya gargadi Amurka game da gabatar da “bukatun da ba su dace ba” a tattaunawar dake tsakanin kasashen biyu, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta ci gaba da inganta sinadarin Uranium tare da ko ba tare da wata yarjejeniya da Washington ba.

Abbas Araghchi na mayar da martani ne ga furucin da manzon shugaban kasar Amurka a yankin Steve Witkoff ya yi cewa, Washington ba za ta bar Iran ta samu karfin sarrafa sinadarin Uranium ba, ko da kashi 1%.

Mista Araghchi, wanda shi ne babban mai shiga tsakani na Iran, ya shaida wa manema labarai cewa, irin wadannan kalamai sun kauce wa tattaunawar.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa Tehran a shirye take ta nuna cewa ba ta da niyyar kera makaman kare dangi idan Amurkawa suka so.

A wata hira da gidan talabijin na ABC na “Wannan Makon,” Witkoff ya ce “Jan layi” na gwamnatin Trump a tattaunawar nukiliya da Iran shi ne cewa Tehran ba ta da ikon inganta makamashin Uranium.

“Idan Amurka na son tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makaman nukiliya ba, yarjejeniya tana kan gaba, kuma a shirye muke mu shiga tattaunawa mai mahimmanci don cimma matsaya da za ta tabbatar da wannan sakamako a cikin dogon lokaci.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya ce nan ba da jimawa ba za a gudanar da zagaye na gaba na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mujallar “Foreign Policy”Ta Amurka: Isra’ila Ba Ta Yi Nasara A Yaki Da Iran Ba

Jaridun kasar Amurka sun bayyana cewa; Isra’ila ta kasa cimma manufofin da ta ayyana a yaki da Iran, sannan kuma ta kara zama saniyar ware a duniya.

Mujallar “Foreign Policy” ta yi ishara da sakamakon yakin da take cewa, ya zamarwa Amurka da kawarta   Isra’ila juyewar reshe da mujiya,domin harin da su ka kai wa Shirin Iran na Nukiliya bai iya kawo karshensa baki daya,maimakon haka ma sai ya jazawa Tel Aviv asarar mai yawa da kuma karfafa kishin kasa a tsakanin Iraniyawa.”

Har ila yau, rahoton mujallar ta “”Foreign Policy” ya ci gaba da cewa; Asarar da aka yi a Isra’ila, tana firgitarwa”,amma a cikin Iran babu cikakken bayani akan girman barnar da aka yi- da hakan yake a  matsayin tsaka mai yuwa ta fuskar muhimman manufofin da Isra’ilan ta so cimmawa da kuma kawarta Amurka.”

Bugu da kari mujallar ta “Foreign Policy” ta ce; Babu wanda yake gaskata abinda Isra’ila take fada na cewa ta rusa Shirin makamashin Nukiliyar Iran,domin hukumomin leken asiri na turai suna cewa, dukkanin sanadarorin kera makaman Nukiliya suna nan kalau ba abinda ya same su.”

Wani sashe na rahoton ya ce; HKI ba ta iya samar da kandagarko na Nukiliya a yakinta da Iran ba,maimakon hakan ma, abu ne mai yiyuwa harin da Isra’ilan da Amurka su ka kai wa Iran ya ba ta karfin gwiwar yin tunanin samar da makamin Nukiliya” a fadar wannan mujalla.

Iran dai ta sha bayyana cewa; Shirinta na sulhu ne, ba kuma wanda yake da hakkin hana ta cin moriyar alfanu mai yawa dake cikin fasahar makamashin Nukiliya.  

Rahoton ya kuma ce; gwamnatin Amurka ta fake da dalilai na karya wajen kai wa Iran hari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • Mujallar “Foreign Policy”Ta Amurka: Isra’ila Ba Ta Yi Nasara A Yaki Da Iran Ba
  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
  • Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi