HausaTv:
2025-06-16@07:08:42 GMT

Iran : zamu ci gaba da inganta uranium ko da yarjejeniya ko babu

Published: 19th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya gargadi Amurka game da gabatar da “bukatun da ba su dace ba” a tattaunawar dake tsakanin kasashen biyu, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta ci gaba da inganta sinadarin Uranium tare da ko ba tare da wata yarjejeniya da Washington ba.

Abbas Araghchi na mayar da martani ne ga furucin da manzon shugaban kasar Amurka a yankin Steve Witkoff ya yi cewa, Washington ba za ta bar Iran ta samu karfin sarrafa sinadarin Uranium ba, ko da kashi 1%.

Mista Araghchi, wanda shi ne babban mai shiga tsakani na Iran, ya shaida wa manema labarai cewa, irin wadannan kalamai sun kauce wa tattaunawar.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa Tehran a shirye take ta nuna cewa ba ta da niyyar kera makaman kare dangi idan Amurkawa suka so.

A wata hira da gidan talabijin na ABC na “Wannan Makon,” Witkoff ya ce “Jan layi” na gwamnatin Trump a tattaunawar nukiliya da Iran shi ne cewa Tehran ba ta da ikon inganta makamashin Uranium.

“Idan Amurka na son tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makaman nukiliya ba, yarjejeniya tana kan gaba, kuma a shirye muke mu shiga tattaunawa mai mahimmanci don cimma matsaya da za ta tabbatar da wannan sakamako a cikin dogon lokaci.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya ce nan ba da jimawa ba za a gudanar da zagaye na gaba na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba

Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.

Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.

Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida